Wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne suka kai hari a makarantar sakandaren mata ta kwana a Dapchi jihar Yobe da ke arewa maso yammacin Najeriya.
'Yan Najeriya sun yi ta murna da farin ciki sakamakon sako 'yan matan makarantar sakandaren Dapchi da Boko Haram ta sace, ta kuma dawo da su ranar 21 ga watan Maris.
An mayar da yaran garinsu ne a ranar Laraba da misalin karfe 3 na tsakar dare.
Sai dai har yanzu akwai sauran yarinya daya mai suna Leah Sharibu, da mayakan kungiyar ba su mayar da ita ba, tana hannunsu.
Amma kuna da labarin duk abun da ya faru tun farkon lamarin?
Kuna iya duba wannan kalandar da ke kasa tare da ci gaba da latsa gaba don samun cikkkun labarai da rahotannin yadda abubuwa suka yi ta wakana.
Wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne suka kai hari a makarantar sakandaren mata ta kwana a Dapchi jihar Yobe da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da sace 'yan Mata 110.
Gwamnatin Yobe ta sanar da cewa sojojin Najeriya sun bi 'yan Boko Haram tare da kwato daliban.
Gwamnatin Yobe ta yi amai ta lashe inda ta nemi afuwa kan sanarwar da ta bayar cewa sojoji sun ceto 'yan matan Dapchi.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bayyana sa ce 'yan matan sakandaren Dapchi a matsayin wani bala'i da ya shafi kasa baki daya.
Rundunar Sojin sama ta sanar da tura jiragen yaki da karin dakaru domin bincike da kuma ceto 'yan matan da aka sace.
An samu sa'insa tsakanin Sojoji da 'Yan sanda kan wadanda alhakin tsaron Dapchi ya rataya a kan wuyansu, inda 'yan sanda suka ce ba da saninsu sojoji suka fice ba.
Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti na mutum 12 domin binciken yadda aka sace 'yan matan Dapchi 110.
Majalisar wakilai ta kafa kwamiti domin gudanar da bincike game da yadda aka sace 'yan matan sakandaren garin Dapchi.
Shugaba Buhari ya ce gwamnatinsa ta zabi ta sasanta da Boko Haram maimakon yin amfani da karfin soja domin ceto 'yan matan a raye.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ziyarci garin Dapchi da ke jihar Yobe a arewa maso gabashin kasar.
Kafar yada labarai ta Amurka ta Wall Street Journal, WSJ, ta ce ta samu bayanan da suka tabbatar mata da cewa bangaren Abu Musab Abu Musab al-Barnawi ne suka sace 'yan matan 110.
Amnesty International ta zargi sojojin Najeriya da yin biris da gargadin cewa 'yan Boko Haram za su kai hari sa'o'i kalilan gabannin a sace 'yan matan sakandaren Dapchi sama da 100, zargin da sojojin suka musanta.
Iyayen 'yan Matan Dapchi sun sanar da sako 'ya'yansu da Boko Haram ta sace.
Gwamnatin Najeriya ta musanta cewa ta biya kudin fansa domin a saki 'yan Matan makarantar sakandaren garin Dapchi da Boko Haram ta sace.