Gane Mini Hanya: Ina PDP, amma zan yi aiki da haɗakar kayar da Tinubu - Sule Lamiɗo
Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamiɗo ya ce yadda ya san halin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a kan cika burin da ya sa a gaba, na cikin abubuwan da suka ƙara masa ƙaimi wajen shiga sabuwar haɗakar ƴan hamayya ta ADC.
Ya ce ya amince ya yi aiki da haɗakar ne a wani yunƙuri na kawar da gwamnatin Tinubun a babban zaɓen ƙasar mai zuwa.
Sai dai a ɓangare guda Sule Lamido, ya ce ba zai fita daga jam'iyyarsa ta PDP ba - wani salo da ke ƙoƙarin zamewa ruwan dare a siyasar Najeriyar a baya-bayan nan.
A zantawarsa da wakilinmu na Kano, Zahraddeen Lawan cikin filinmu na Gane Mini Hanya a wannan mako, tsohon gwamnan Jigawa ya fara ne da yin waiwaye kan abin da yake gani shi ne mafari na halin da siyasar Nijeriya ta samu kanta ciki.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai