'Nigeria ba ta da tsarin tattalin arziki'

Masana tattalin arziki a Najeriya sun ce kasar ba ta da tsarin tattalin arzikin kasa na gajere da matsakaici da kuma dogon zango.
Dr. Nazifi, malami ne a jami'ar Abuja ya alakanta matsalolin da kasar take fuskanta sakamakon rashin tsarin da kasar take da shi.
Sai dai kuma masanin ya shawarci gwamnatin kasar da ta kira masanan a tsara sabon kundin tsarin tattalin arzikin kasar.
A ranar Litinin din nan ne dai Majalisar Tattalin Arzikin Najeriyar ta za ta fara wani taro na kwanaki biyu da nufin tattaunawa a kan matakan da ya kamata gwamnatocin tarayya da jihohi su dauka don zaburar da tattalin arzikin su.
Alhakin majalisar dai,shi ne bai wa shugaban kasa shawara a kan al'amuran da suka shafi tattalin arzikin kasa.
Mataimakin shugaban kasaR, Prof. Yemi Osinbajo ne yake jagoranta majalisar, ta kuma kunshi gwamnonin jihohin kasar 36.






