Yadda ta kaya a gasar kofin FA
Manchester City ta yi nasarar tsallakewa zuwa zagaye na hudu na gasar cin Kofin Kalubale, bayan da ta doke Port Vale da ci 4-1.
City ta lashe duka kofuna hudu na cikin gida a bara, to amma a bana tana fuskantar babban kalubale a gasar Firimiya daga Liverpool.
City ta saka wa bakin kwallayen hudu ne ta hannun Phil Foden da Sergio Aguero da kuma Oleksandr Zinchenko.
A minti na 58 ne kuma dan wasan Port Vale Taylor Harwood-Bellis ya ci gida.
To sai dai makwabtan City din wato Manchester United wadda a baya ta lashe kofin na FA sau goma sha daya ta yi canjaras ba ci 0-0 da Wolverhampton.
A karon farko cikin shekara biyar, United ta kammala wasa ba tare da buga wa mai tsaron raga kwallon da ya ture ba.
Ita ma Leicester ta doke Wigan ne 2-0, yayin da Bournemouth ta casa Luton 4-0
Ga dai yadda sakamakon kungiyoyin da ke Firimiya ya kasance.
Wolves 0-0 Manchester United
Preston 2-4 Norwich
Burnley 4-2 Peterborough
Southampton 2-0 Huddersfield
Bournemouth 4-0 Luton
Leicester 2-0 Wigan
A ranar Lahadi Liverpool za ta karbi bakuncin makwabciyarta Everton a ci gaba da gasar cin kofin na kalubale.
To sai dai kafin nan Chelsea za ta kara da Nottingham Forest, inda Tottenham za ta kece raini da Middlesbrough.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai