Me ya faru a yakin neman zaben Buhari da na Atiku? Hotunan Afirka a makon jiya

Mun zabo muku hotunan wasu abubuwan da suka faru a Afirka da 'yan Afirka a wasu wuraren a makon jiya.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Ranar Lahadi a birnin Los Angeles, mambobin kungiyar mawakan coci ta the Soweto Gospel Choir sun dauki hoto bayan sun lashe kyautar Grammy.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Mawakiya 'yar kasar Mali Fatoumata Diawara ta cashe a ranar, a wurin bikin ba da lambar yabon ta Grammy inda aka sanya hotuna, ciki har da na dalar Masar.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Ranar Juma'a, mawakiya 'yar kasar Uganda Jackie Akello, sanye da tufafi masu launin ruwan goro, ta bi sahun sauran jama'a a wurin bikin the Sauti za Busara...

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, An gudanar da bikin ne, wanda ake yi duk shekara, a Stone Town da ke yankin Zanzibar na kasar Tanzania...

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, 'Yan kallo sun je daga sassa daban-daban na Tanzania da kuma nahiyar Afirka domin su kashe kwarkwatar idanunsu.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Wannan yaron yana yin rawa a wani wurin taro da ke jihar Adamawa ta Najeriya gabanin gangamin yakin neman zaben da jam'iyyar hamayya ta Peoples Democratic Party ta yi ranar Alhamis a wurin.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Ranar Talata, mutum 15 ne suka mutu sakamakon turmutsutsu da aka yi a wajen gangamin yakin neman zaben Shugaba Buhari na jam'iyyar APC a birnin Port Harcourt. An dauki wannan hoton ne kwana daya bayan faruwar wannan iftila'i

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Ranar 16 ga watan Fabrairu aka so gudanar da zabuka a Najeriya. Wasu masu kantuna sun ce shirye-shiryen zabukan sun hana su yin ciniki sosai domin zagayowar ranar Masoya ta duniya inda ake sayen irin wadannan kayan da ake bai wa masoya kyautuka.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, An shirya wadannan furanni ne a Kenya ranar Talata domin kai su ga masu bikin zagayowar ranar Masoya ta Duniya...

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Kenya ce kasa ta uku da ke fitar da irin wadannan furanni zuwa kasashen duniya, a cewar wasu alkaluma daga ofishin kididdiga.

Asalin hoton, Anadolu Agency

Bayanan hoto, Ranar Lahadi, an kaddamar da mutum mutumin Sarkin Daular Habasha, Haile Selassie a hedikwatar Tarayyar Kasashen Afirka da ke birnin Addis Ababa na Ethiopia. Lokacin mulkinsa, ya taimaka wajen kafa Kungiyar Hada kan Kasashen Afirka.

Asalin hoton, Anadolu Agency

Bayanan hoto, Ranar Asabar, an nada Sabrine Khalifa Mansour a matsayin sarauniyar kyau ta Tunisia ta shekarar 2019 a bikin da aka yi a birnin Tunis.

An samu wadannan hotuna ne daga kamfanonin dillancin labaran AFP, Anadolu Agency da kuma Getty Images