KAI TSAYE, Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 01/04/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 01 ga watan Afrilun 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga AishaBabangida da Haruna Kakangi

  1. As sake mayar da El-Rufai kotu don sauraron neman beli

    ...

    Asalin hoton, El-Rufai/X

    Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya sake gurfana a gaban babbar kotun tarayya da ke Kaduna domin ci gaba da sauraron buƙatarsa ta neman beli.

    Tsohon gwamnan ya isa kotun da misalin ƙarfe 9 na safe a ranar Laraba, cikin tsauraran matakan tsaro.

    Ci gaba da sauraron shari’ar ya biyo bayan ɗage zaman da mai shari’a, Rilwan Aikawa ya yi a ranar Talata, sakamakon wasu sabbin matakan shari’a tsakanin ɓangaren masu kare shi da kuma masu gabatar da ƙara.

    Lauyoyin El-Rufai, ƙarƙashin jagorancin Ubong Akpan, sun fara shigar da buƙatar neman mai shari’ar ya janye daga shari’ar bisa zargin nuna son kai, amma daga baya suka janye wannan buƙata, lamarin da ya janyo jinkiri a tafiyar da shari’ar.

    A ɓangaren masu gabatar da ƙara kuwa, sun shigar da hujjar da ke adawa da bayar da belinsa wanda ya bar ɓangaren masu kareEl-Rufai da ƙarancin lokaci na mayar da martani, abin da ya sa aka ɗage shari’ar zuwa Laraba domin ci gaba.

    A makon da ya gabata ne hukumar ICPC ta gurfanar da shi a gaban mai shari’a Rilwan M. Aikawa kan tuhume-tuhume guda 10 da suka haɗa da zargin karkatar da kadarorin gwamnati da kuma halasta kuɗaɗen haram

  2. An sassauta dokar hana zirga-zirga a unguwar Rukuba da ke Jos

    ....

    Asalin hoton, X/Caleb Mutfwang

    Gwamnatin jihar Filato ta sassauta dokar hana zirga-zirga da aka sanya a Unguwar Rukuba ta Jos ta arewa bayan harin ranar 29 ga Maris da ya kashe aƙalla mutane 27.

    “An fara wannan sassautawar ne daga ranar 1 ga Afrilu, 2026, inda ake ba da damar zirga-zirga daga ƙarfe 7:00 na safe zuwa 3:00 na yamma a kullum. An yi kira ga mazauna unguwar da su yi amfani da wannan lokacin wajen gudanar da ayyukan da suka dace da doka tare da bin ƙa’idojin tsaro,” in ji kwamishinan labarai na jihar, Joyce Ramnap.

    Gwamnatin jihar ta ce jami’an tsaro za su ci gaba da gudanar da sa ido da sintiri don tabbatar da zaman lafiya da hana ɓarkewar tashin hankali.

    Da farko dai, gwamnati ta sanar da sanya dokar hana zirga-zirga na sa’o’i 48 bayan harin da ‘yan bindiga suka kai a Angwan Rukuba.

    Sai dai mazauna unguwar, cikin fushi, sun karya dokar hana zirga-zirgar inda suka fita kan tituna don zanga-zangar nuna rashin jin daɗi da kuma neman gwamnati ta ɗauki mataki kan tashin hankali da ake fuskanta a jihar a kai a kai.

    Filato, wanda ke tsakiyar Najeriya, na fuskantar rikice-rikice akai-akai tsakanin makiyaya da manoma kan haƙƙin amfani da ƙasa da ruwa.

  3. Harin Iran a Isra'ila ya jikkata mutum 14

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni daga hukumomin Isra’ila sun ce wani hari da Iran ta kai da makami mai linzami a Tel Aviv a yau ya jikkata mutum 14..

    Ba a samu rahoton cewa harin ya lalata wurare ba lalacewa amma hukumomin agajin gaggawa na Isra’ila sun ce mutum goma sha huɗu sun jikkata sakamakon hare-haren a unguwannin da ke kusa da Tel Aviv.

    A safiyar yau, an yi kira ga mazauna wasu yankuna a tsakiyar Isra’ila, ciki har da Tel Aviv, su nemi mafaka sau da dama.

    Hukumomin Isra’ila sun ce mutum 19 ne suka mutu tun farkon rikicin, mafi yawansu sakamakon ƙananan ɓirɓishin makaman masu linzami da aka kakkaɓo

  4. Ana ci gaba da musayar wuta tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun ce an sake yi wa Iran ruwan bama-bamai, inda rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kammala abin da ta kira wasu jerin hare-hare ta sama a kan wuraren da ta ce na gwamnatin Iran din ne, a babban birnin ƙasar, Tehran.

    A cikin dare rundunar sojin Amurka ta fittar da wani bidiyo da ke nuna sojojinta na jefa abin da ta kira bama-bamai na yankan-shakku a wuraren da ta ce na soji ne da ke karkashin kasa.

    Kamar dai yadda aka saba, ita ma Iran din ba ta sarara ba a martanin da take kai wa, inda jamiai a Kuwait suka ce wuta ta tashi a babban filin jirgin sama na kasar, sakamakon harin jirgin sama maras matuki da Iran ta kai a kan wasu tankunan mai.

    Can a Bahrain Iran din ta kai hare-hare cikin dare inda gobara ta tashi .

    Haka kuma hukumar jamian tsaro na teku ta Birtaniya ta ce wani makami mai linzami ya fada kan wani jirgin ruwa na dakon mai a gabar tekun Qatar

  5. Iran ta kai wa tankar man Qatar hari da makami mai linzami

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar tsaron Qatar ta sanar da cewa Iran ta kai mata harin makamai mai linzami kan tankar man ta a ranar Laraba.

    Iran ta kaddamar da hare-haren makamai masu linzami guda uku, amma Qatar ta ce ta kakkaɓo biyu daga ciki, inda na ukun ya sauka kan tankar man ta, ta Aqua-1.

    Sai dai ba a samu asarar rai a harin ba.

    Hukumar kula da sufurin jiragen ruwa ta Birtaniya da hukumar kula da makamashin Qatar, sun ce harin ya lalata jirgin da ke cikin tekun ta a arewacin Ras Laffan.

    Matatar iskar gas mafi girma a duniya tana yankin Ras Laffan ne a ƙasar Qatar, amma an rufe ta saboda hare-haren Iran.

  6. Za mu kawo ƙarshen yaƙin Iran ko da yarjejeniya ko babu - Trump

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya nuna cewa yana son ya rage hare-haren da ake kai wa Iran, yana mai alƙawarin cewa yaƙin zai zo karshe a cikin mako biyu ko uku masu zuwa ko da an cimma yarjejeniya ko ba a cimma ba.

    Ya ce yanzu Iran tana da sababbin shugabanni waɗanda suka fi sauƙin samu, ba masu tsattsauran ra'ayi ba kuma wadanda suka fi magabatansu hankali.

    Ya ce gwamnatin Amurka ta cimma burinta, duk da cewa ba ta iya kwace mashigar Hormuz ba daga hannun Iran. Yuwuwar ci gaba da karancin mai, farashin danyen man ya kara tashi a yau Laraba.

    To amma kuma Mista Trump ya ce nan gaba kadan farashin zai sauka. A yau zai gabatar da jawabi ga al'ummar kasar ta Amurka ta talabijin.

  7. Haɗakar ADC : Wane tasiri shigar manyan ƴan'adawa za ta yi a zaɓen 2027

    ....

    Asalin hoton, BBC Collage

    Bisa ga dukkan alamu a Najeriya an kama hanyar gina babbar hadaka ta siyasa gabanin babban zaben kasar na 2027, bayan shigar tsohon gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso jam'iyyar ADC.

    Ana kallon hadewar Kwankwaso da tsohon mataimakin shugaban kasar, Atiku Abubakar da kuma Peter Obi, wadanda dukkaninsu sun tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2023, a matsayin wani babban ci gaba a bangaren hamayya a Najeriya, kuma wani babban kalubale ga jam'iyya mai mulki.

    Yayin da ake ganin cewa siyasar hamayya a Najeriya tamkar ta shude - ganin yadda ake ta sauya sheka zuwa APC mai mulki, wasu masana na ganin wannan sabuwar hadaka ta jam'iyyar ta ADC ka iya zama wani babban kalubale ga Shugaba Tinubu da jam'iyyarsa ta APC a zaben 2027.

    Haka kuma masanan na ganin siyasar hamayya a kasar wadda ta fi yawan jama'a a Najeriya za ta sake farfadowa fiye da yadda ba a zata ba.

  8. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba ga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.