As sake mayar da El-Rufai kotu don sauraron neman beli

Asalin hoton, El-Rufai/X
Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya sake gurfana a gaban babbar kotun tarayya da ke Kaduna domin ci gaba da sauraron buƙatarsa ta neman beli.
Tsohon gwamnan ya isa kotun da misalin ƙarfe 9 na safe a ranar Laraba, cikin tsauraran matakan tsaro.
Ci gaba da sauraron shari’ar ya biyo bayan ɗage zaman da mai shari’a, Rilwan Aikawa ya yi a ranar Talata, sakamakon wasu sabbin matakan shari’a tsakanin ɓangaren masu kare shi da kuma masu gabatar da ƙara.
Lauyoyin El-Rufai, ƙarƙashin jagorancin Ubong Akpan, sun fara shigar da buƙatar neman mai shari’ar ya janye daga shari’ar bisa zargin nuna son kai, amma daga baya suka janye wannan buƙata, lamarin da ya janyo jinkiri a tafiyar da shari’ar.
A ɓangaren masu gabatar da ƙara kuwa, sun shigar da hujjar da ke adawa da bayar da belinsa wanda ya bar ɓangaren masu kareEl-Rufai da ƙarancin lokaci na mayar da martani, abin da ya sa aka ɗage shari’ar zuwa Laraba domin ci gaba.
A makon da ya gabata ne hukumar ICPC ta gurfanar da shi a gaban mai shari’a Rilwan M. Aikawa kan tuhume-tuhume guda 10 da suka haɗa da zargin karkatar da kadarorin gwamnati da kuma halasta kuɗaɗen haram






