'Za mu yaki kungiyar IS' - al-Shabaab
Asalin hoton, AFP
Kungiyar al-Shabaab ta kasar Somaliya ta ce za ta yaki kungiyar IS da ke cikin kasar.
Kakakin kungiyar Sheikh Ali Rage ne ya bayyana haka a cikin wata hira da ya fitar, inda ya yi kira ga mayakan kungiyar al-Shabaab su kai hare-hare 'har sai sun shafe mayakan IS daga kasar'.
Duk da yake bangarorin biyu sun sha gwabza fada a wasu sassa na Somaliya a watannin baya bayan nan, wannan ne karo na farko da al-Shabaab ta fitar da irin wannan jawabin.
Kakakin kungiyar al-Shabaab ya saki sako na sautin muryarsa mai tsawon minti 42 a shafukan kungiyar na sada zumunta.
Kakakin kungiyar Sheikh Ali Rage ya zargi kungiyar IS da "kawo cikas ga yakin jihadin da ake yi a Somaliya".
Ya kuma kira kungiyar ta IS a matsayin "wata muguwar cuta" kuma "cutar daji", kuma ya kira mayakan al-Shabaab da su yaki kungiyar ta IS a kasar.
Da alama wadannan kalaman na mayar da martani ne ga ikirarin da IS ta yi cewa mayakanta sun kashe wasu mayakan al Shabaab a yankin Puntland.
Kungiyoyin biyu sun sha gwabza fada tun bayan da IS ta bayyana a Somaliya, inda ta kafa sansanoninta a arewacin kasar, kuma ta fara karbar kudin kariya daga 'yan kasuwan kasar, kamar yadda rahotanni daga kafafen watsa labarai suka ruwaito.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai