Duk wanda bincike ya biyo ta kansa ba zai sha ba - Malami

Ministan shari'a na Najeriya, Abubakar Malami ya ce idan har bincike kan rashawa da cin hanci ya tarar da tsohon Shugaban kasar, Goodluck Jonathan, babu makawa za a iya bincikar sa.

Malami ya ce aikin binciken masu laifi karkashin shugabancin Shugaba Muhammadu Buhari babu zabe a ciki.

Abubakar Malami ya bayyana haka a kashi na biyu na hirar da editanmu na Abuja, Naziru Mika'ilu ya yi da shi.

Ku saurari yadda hirar tasu ta kaya.