Za a yi bikin gwarazan Afrika a birnin Marrakesh na Moroko
Asalin hoton, CAF
Hukumar kwallon ƙafa ta Afrika CAF ta sanar da cewa za a gabatar da bikin kyautar gwarazan Afrika ta 2024 a birnin yawon buɗe ido na Marrakesh da ke Moroko.
An tsara za a gudanar da kyautar ne a ranar 16 ga watan Disambar 2024.
Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, CAF ta sanar da cewa lokaci ya sake zagayowa.
"Shekara ta ƙara zagayowa. #CAFaward2024. Disamba 16 ga wata a Marrakesh Maroko. Kusa a kalandarku."
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Wannan ne karo na biyu a jere da ake gudanar da bikin a birnin na Marrakesh, karo na uku kuma da ake yi a Moroko.
CAF za ta tabbatar da lokacin da za a fara kyautar ta 2024 da zarar lokaci yayi.
Wanda ke rike da kambun kyautar ta ɓangaren maza shi ne ɗan wasan Najeriya na gaba, Victor Osimhen.
A ɓangaren mata kuwa takwararsa da Najariya Asisat Oshoala ce ke riƙe da kyautar.
Kyautar tana mayar da hankali ne kan ƙoƙarin da 'yan wasa ke yi a ƙasarsu da kuma ƙungiyoyin da suke bugawa ƙwallo, domin bayar da wannan kyauta mai daraja ta gwarazan Afrika ɓangaren maza da mata ta shekara.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai