Boko Haram 'ta kafa tuta' a wasu kauyuka uku a Borno
Asalin hoton, Getty Images
Wata majiyar soji da fararan hula na cewa mayakan Boko Haram sun kafa tutocinsu a wasu kauyuka uku a jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Nigeria.
Mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa mayakan sun yanka mutane takwas, ciki har da wani dagaci, a lokacin da suka hare-haren a yammacin ranar Litinin.
Kauyukan na Kubirivour, Boftari and Kuburmbalah na kusa da garin Chibok ne, inda aka sace 'yan makaranta fiye da 200 a 2014.
Akalla mutane 17 ne aka jikkata a hare-haren.
Wata majiya ta ce har yanzu mayakan Boko Haram na rike da garin Malam Fatori, wanda ke kan iyakar Najeriya da Nijar.
A ranar Lahadi ne, sojojin Najeriya suka kwato garin daga hannun mayaka.
Sai dai rahotanni sun ce sun sake damara inda suka sake kwace iko da garin.
Wakilin BBC a Najeriya ya ce hare-haren na baya-bayan nan na nuna yadda har yanzu kungiyar ta Boko Haram ke ci gaba da zama barazana ga kasar.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai