Man City ta rage tazara tsakaninta da Liverpool
Asalin hoton, Getty Images
Manchester City ta yi nasarar doke West Ham United da ci 2-0 a kwantan wasan mako na 26 da suka kara a Etihad.
Tun farko karawar ta zama kwantai bayan da rashin kyawun yanayi ya sa aka dage fafatawar ta su.
City ta fara cin kwallo ne ta hannun Rodri saura minti 15 a je hutun, bayan hutun ne City ta kara na biyu ya hannun Kevin de Bruyne.
Karo na uku kenan Rodri na ci wa City kwallo kuma na farko a filin wasa na Etihad.
Kuma kungiyar kwallon kafa ta Aston Villa aka ci kwallo tara da ka a tarihin Premier bana, sai West Ham mai guda takwas.
Da wannan sakamakon City ta rage tazarar maki da ke tsakaninta da Liverpool ta daya a teburi daga 25 yanzu ya koma 22.
West Ham tana nan a mataki na 18 da maki 24, bayan buga wasan Premier 26.
Asalin hoton, BBC Sport
City za ta ziyarci Leicester City a wasan mako na 27 a gasar ta Premier ranar 22 ga watan Fabrairu.
Ita kuwa West Ham United za ta ziyarci Liverpool ne ranar Litinin 24 ga watan Fabrairu.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai