Mun mayar da Sokoto birnin yawon buɗe ido - Aliyu

Asalin hoton, Sokoto State Government
Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya bayyana cewa aiki ne a gabansa, shi ya sa sukar da yake sha daga wasu mutane ba za su hana shi gudanar da ayyukan ci gaban jihar ba.
Gwamnan ya bayyana haka ne lokacin taron bude-baki da shugabannin kungiyar ‘yan kasuwa na jihar a ranar Alhamis.
Aliyu, wanda ya bayyana cewa gwamnatinsa ta kammala shirin bayar da bashi ga ‘yan kasuwa da zaran an kammala gyaran wani bangare na kasuwar Sokoto da gobara ta lalata, ya ce a shirye yake ya tallafa wajen bunkasar harkokin kasuwanci a jihar.
A cikin sanarwar da ya fitar ta hannun daraktan yada labarai da hulda da jama’a, Abubakar Bawa, Gwamna Aliyu ya ce “ci gaban da muka samar a bayyane yake, ta ko ina. Misali, yadda ake mayar da birnin Sokoto wurin yawon bude ido.
“Mun fahimci cewa mutane daga wasu wurare suna zuwa da daddare domin kallon birnin har ma suna daukar hotuna,” in ji Aliyu.
Daga nan ya ce gwamnatinsa na maraba da suka mai ma’ana daga mutane masu fatan alheri.



















