Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 26 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Gwamnatin Jigawa ta karɓi Walida Abdulhadi

    Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi

    Asalin hoton, FB/Umar Namadi

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi

    Gwamnatin jihar Jigawa ta sanar da cewa an miƙa mata matashiyar nan mai suna Walida Abdulhadi, wadda ake zargin wani jami'in rundunar tsaro ta farin kaya (DSS) da "ajiye ta a wurin shi" na tsawon shekaru.

    A wata tattaunawa da BBC a yammacin yau Alhamis, kwamishinan yaɗa labarai na jihar Sagir Musa ya ce an miƙa matashiyar ga gwamnatin Jigawa ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Alhamis.

    Kwamishinan ya bayyana cewa a daren ranar jiya Laraba ne gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya samu sahhalewar shugabannin hukumar DSS domin karɓar matashiyar.

    "Da rana, ƙarfe biyu mai girma gwamna ya kira shugaban DSS, sannan ya tura wakilci ƙarƙashin kwamishinan shari'a a na jihar da kwamishinar mata da kuma sakataren yaɗa labaran gwamnan, suka je ofishin DSS, kuma a yanzu maganar da muke yi zan iya tabbatar muku cewa wannan yarinya tana ƙarƙashin kulawar gwamnatin Jigawa," in ji Sagir.

    Ya ƙara da cewa ya zuwa yammacin Alhamis Walida tana Abuja, inda za a kai ta asibiti domin duba lafiyarta.

    An kwashe makonni ana kai-komo game da batun matashiyar, wadda kotu ta bayar da umarnin miƙa ta ga iyayenta.

    Lauyoyin da suka shiga batun sun zargi jami'in na DSS da "sacewa tare da yin kwanciyar aure da matashiyar har ta haifa masa ɗa".

  2. An ci gaba da takun saƙa tsakanin Guinea da Sierra Leone

    ...

    Zaman ɗar-ɗar ya ƙaru tsakanin Guinea da Sierra Leone bayan kama sojojin Sierra Leone guda 16 kan zargin shiga ƙasar Guinea ba bisa ƙa’ida ba kamar yadda rahotannin kafofin watsa labarai na Guinea suka ruwaito.

    An bayar da rahoton cewa rundunar sojin Guinea ta ce sojojin sun shiga ƙasar a gundumar Koudaya dake cikin babban yankin Faranah, kusan kilomita 1.4 cikin ƙasar Guinea, inda suka kafa tantuna tare da ɗaga tutar ƙasarsu.

    Sojojin Guinea sun kai farmaki inda suka kama sojojin, suka ƙwace makamai da kayan su, wanda daga bisani aka miƙa wa ƴan sandan shari’a don gudanar da bincike.

    Sai dai kuma gwamnatin Saliyo ta musanta wannan batu, inda ta ce sojojin Guinea ne suka tsallaka zuwa garin Kaliyereh da ke gundumar Falaba a ranar 23 ga watan Fabrairu, inda jami'an Saliyo ke jibge.

    Ta kuma ce an tsare da yawa daga cikin jami’ansa inda aka shigar da su cikin Guinea, tare da ƙwace makamansu.

    Gwamnatin ƙasar ta ce ta fara gudanar da ayyukan diflomasiyya don ganin an sako sojojin cikin "aminci kuma ba tare da wani sharaɗi" ba.

  3. Firaministan Denmark ta kira zaɓe yaiyin da batun Greenland ke ci gaba da tayar da ƙura

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Firaministan ƙasar Denmark Mette Frederiksen ta sanar da zaɓukan gaggawa inda ta bayyana shekara huɗu masu zuwa a matsayin "masu muhimmanci" ga ƙasarta.

    A ƴan watannin da suka gabata shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar mamaye yankin Greenland – wani yanki mai cin gashin kansa na Denmark.

    A watan da ya gabata, Trump ya yi watsi da barazanar amfani da ƙarfi kan abokan ƙawancen NATO don ƙwace tsibirin Arctic da ya ce ya zama dole don kare hare-hare daga Rasha da China.

    Da ta ke sanar da yanke shawarar kiran zaɓen da wuri a ranar 24 ga Maris, Firaminista Frederiksen ta shaida wa majalisa cewa tsaro "shine kuma zai kasance ginshikin siyasar Denmark na shekaru da dama masu zuwa".

  4. An zargi ma'aikatar shari'a ta Amurka da ɓoye bayanan Epstein da ke da alaƙa da Trump

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Babban dan jam'iyyar Democrat a kwamitin majalisar wakilai da ke binciken Jeffrey Epstein ya zargi ma'aikatar shari'a ta Amurka da riƙe wasu bayanan da ke ɗauke da zargin cin zarafin wata ƙaramar yarinya da aka yi wa Shugaba Donald Trump.

    Robert Garcia, wanda mamba ne na kwamitin sa ido na majalisar, ya ce shi da kansa ya kalli takardun da ke kunshe da zargin da ba a bayyana ba.

    A martanin da ma’aikatar shari’ar ta mayar ta ce, “Babu wani abu da aka goge”, ta kuma ƙara da cewa an riƙe takardun ne kawai idan “na kwafi ne, ko kuma sun shafi wani ɓangare na binciken da gwamnatin tarayya ke yi”.

    Trump ya sha musanta aikata wani laifi dangane da batun Epstein kuma a kwanan baya ya ce an “wanke shi baki ɗaya”.

    A baya ma'aikatar shari'ar ta kuma ce wasu daga cikin bayanan na ɗauke da zarge-zargen ƙarya kan Shugaba Trump".

  5. An sake samun raguwa a yawan jariran da ake haihuwa a japan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An sake samun raguwa a yawan jariran da ake haihuwa a kasar japan a cikin shekara goma a jere.

    Ma’aikatar lafiya ta kasar ta ce jarirai fiye da dubu dari bakwai aka haifa a bara abinda ke nuni da cewa an samu raguwa da kashi biyu da digo daya cikin dari.

    Idan kuma aka cire yan kasashen wajaen da suka haihu a kasar to adadin zai kara yin kasa.

    Wannan komabaya na zuwa ne duk da kokarin da gwamnatin kasar take yi wajan shawo kan matsalar raguwar haihuwa a cikin kasar

  6. Ba mu yarda da dokar zaɓen da Tinubu ya sanya wa hannu ba - Jam'iyyun adawa

    ...

    Shugabannin jam’iyyun adawa a Najeriya sun yi watsi da dokar zaɓe ta 2026 da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rattabawa hannu.

    Shugabannin da manyan jam’iyyun adawa wanda tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya jagoranta sun caccaki yanayin yadda majalisar dokokin ƙasar ta amince da dokar.

    Da yake jawabi ga manema labarai, Ajuri Ahmed na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) ya ce alƙaluman da suke da su sun nuna cewa ana iya yaɗa sakamakon zaɓe daga kowace rumfar zaɓe kuma suna mamakin dalilin da ya sa za a shigar barun shigar da sakamakon zaɓe da hannu cikin dokar.

    Ya ce zaɓen babban birnin tarayya Abuja da aka kammala ya nuna dalilin da ya sa jam’iyyar APC ta yi gaggawar sanya hannu kan dokar zaɓen.

    Shugabannin ƴan adawar sun kuma yi watsi da zaɓen babban birnin tarayya Abuja, inda suka ce zaɓen ƙananan hukumomin jarrabawa ne da sabon shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ya kasa ci.

  7. Ghana ta tattauna batun sakin fursunonin yaƙi biyu daga Ukraine

    ...

    Asalin hoton, GHANA FOREIGN AFFAIRS MINISTRY

    Ghana na tattaunawa da Ukraine domin a sako ƴan ƙasarta biyu da ake tsare da su a matsayin fursunonin yaƙ a ƙasar, bisa dalilan jin kai.

    Ministan harkokin wajen Ghana Samuel Okudzeto Ablakwa ya bayyana ƙwarin gwiwar tattaunawar da aka yi bayan ganawarsa da shugaban ƙasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy.

    Ya ƙara da cewa shugaban ƙasar Ghana John Mahama ya godewa Zelenskyy saboda "tabbatar da cewa an kare haƙƙin ƴan ƙasarmu da ake tsare da su kamar yadda dokokin ƙasa da ƙasa suka tanada".

    Kazalika ƙasashen biyu sun tattauna kan inganta alaƙarsu ta fannin tsaro da kasuwancin da noma da kuma ilimi.

    Rahotannin da ke nuni da cewa ƴan Afirka da ke taya Rasha yaƙi da Ukraine sun ɓullo ne a baya bayan nan, inda aka ce ministan harkokin wajen Ukraine Andrii Sybiha ya ce adadin ya kai sama da 1,700 daga ƙasashe 36.

  8. Hillary Clinton za ta bayyana a gaban kwamitin majalisar dokokin Amurka da ke binciken Epstein

    ...

    A ranar Alhamis ne Hillary Clinton za ta bayyana a gaban wani kwamitin majalisar wakilan Amurka da ke binciken laifukan mutumin nan da aka samu da aikata laifukan jima'i Jeffrey Epstein.

    Kwanan nan tsohuwar sakatariyar harkokin wajen Amurka kuma ƴar takarar shugaban ƙasa ta amince tare da mijinta, tsohon shugaban ƙasa Bill Clinton, don ba da shaida ga kwamitin sa ido na majalisar.

    Dukansu a baya sun ƙi amincewa da buƙatar bayyana a gaba kwamitin, suna masu bayyana lamarin a matsayin bi-ta-da-ƙullin siyasa.

    Hillary Clinton ta ce ba ta tuna ganawa ko magana da Epstein ba.

    Mijinta, wanda ya san Epstein, ya musanta aikata wani laifi ko kuma wata masaniya kan laifukan da ya aikata.

  9. Shugaban ƙungiyar tattalin arziƙin duniya, Borge Brende ya yi murabus

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙungiyar tattalin arzikin duniya, Borge Brende, ya yi murabus saboda alakarsa da marigayi Baamurkenan da aka samu da laifin lalata Jeffrey Epstein.

    A farkon wannan watan ne ƙungiyar ta World Economic Forum ta ce tana gudanar da bincike, bayan wasu takardu da aka fitar a Amurka sun nuna cewa Brende ya ci abincin dare da Epstein, kuma ya aika masa da sako ta email da waya .

    Ƙungiyar ta ce a yanzu ba ta samu wasu abubuwa masu tayar da hankali ba.

    Sanarwar ajiye aiki da Brende ya fitar bata ambaci sunan Epstein ba.

    Ƙungiyar ita ce ke shirya taron tattalin arziki na duniya da ake yi kowace shekara a birnin Davos na ƙasar Switzerland da ke samun halatar shugabannin siyasa da na yan kasuwanci

  10. An kashe mutum 25 a Adamawa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Aƙalla mutum 25 ne aka kashe a wasu hare-hare guda biyu da ake kyautata zaton mayaƙan Boko Haram ne suka kai a jihar Adamawa da ke arewacin Najeriya kamar yadda wasu mazauna yankin suka sanar da kamfanin dillancin labarai ta AFP a ranar Alhamis.

    An kai hare-haren ne a garuruwan Madagali da Hong, dake kan iyaka da ƙasar Kamaru, inda ake danganta su ƙungiyar ‘yan Boko Haram, waɗanda ke kai hare-hare a yankin tun lokacin da ƙungiyar ta fara tashe-tahsen hankula a 2009.

    "Wani rukuni na masu bindiga da muke zaton ‘yan Boko Haram a kan babura ne suka kai hari a kasuwa inda suka buɗe wuta kan mutane, harin da ya kashe mutum 21," in ji wani jami’in gwamnatin ƙaramar hukumar Madagali ga AFP, wanda ya nemi a boye sunansa.

    "Har yanzu muna bincike don neman wasu gawawwakin, saboda wasu na iya mutuwa a cikin daji sakamakon raunukan bindiga yayin da suke kokarin tsira."

    Maharan sun kuma saci kayayyaki a kasuwar da suka haɗa da abinci da babura, in ji shi.

    A garin Hong, mutane hudu sun rasa rayukansu, ciki har da sojoji uku, a cewar mazaunin garin Ezekiel Musa.

  11. Amurka ta yi alla-wadai da harin jirage marasa matuƙa a Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Amurka ta yi allawadai da amfani da jirage marassa matuka da ƴan tawayen RSF a Sudan ke yi kan fararen hula a yaƙin da suke yi da gwamnati.

    Majiyar jami'an lafiya da masu fafutuka sun ce hari irin wannan da aka kai a farkon watan nan ya hallaka mutum 40 ciki har da ƙananan yara.

    Washington ta ce dukkan ɓangarorin biyu, da sojojin Sudan da na ƴan tawayen RSF na aikata mummunan laifi da gallazawa farar hula da ma'aikatan agaji.

    Ofishin ma'aikatar cikin gida kan harkokin Afirka, ya ce yaƙin ya ɗaiɗaita rayuwar farar hula da ba su ji ba ba su gani ba, da suke zaman zullumi da fargabar kowanne lokaci za a iya kai musu harin jirgi marasa matuƙi.

    An samu rahotannin sojoji sun kai hari wata kasuwa, yayin da su ma ƴan tawayen RSF suka kai hari kan wani asibiti a birnin Khartoum da ya hallaka jami'an lafiya.

    Amurkar ta kuma zargi ɓangarorin biyu da amfani da yunwa a matsayin makamin yaƙi, bayan kisan jami'an agaji da ke rabawa farar hula tallafin abinci, sun kuma lalata rumbunan kayan shirin samar abinci na Majalisar Dinkin Duniya.

    A makon da ya gabata wata tawagar masu bincike ta Majalisar Dinkin Duniya ta yanke hukuncin cewa farmakin da RSF ta kai El fasher ya ƙunshi alamomin kisan ƙare dangi.

  12. An binne mutane shida da Lakurawa suka kashe a Kebbi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An yi jana'izar aƙalla masallata shida da aka kashe a wani harin ramuwar gayya da mayaƙan Lakurawa suka kai a masallaci da ke yankin karamar hukumar Maiyama a jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya.

    An kai wa mutanen harin ne yayin suke tsaka da sallar Asham.

    Al’ummar yankin sun ce maharan sun kai harin ne a ranar Laraba a babban Masallacin garin na Dadin Kowa, inda sukai masa ƙawanya sannan suka buɗe wuta tare da jikkata wasu.

    Sai dai hukumomin yankin na cewa suna ɗaukar matakai domin shawo kan matsalar.

    Wani rahoton tsaro da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu ya ce mutum 10 aka kashe a harin.

    Kakakin ‘yan sandan Kebbi, Bashir Usman, bai amsa buƙatar AFP na ƙarin bayani ba nan take, amma ya shaida wa NAN cewa harin ya biyo bayan kashe wasu daga cikin mayakan Lakurawa a wani “yunƙurin kautan ɓauna da suka kai da bai yi nasara ba a kan sojojin Najeriya

    Usman ya ce: "Harin na ramuwar gayya ne daga wasu yanbindiga da ake zargin ƴan kungiyar Lakurawa ne, bayan wani yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan rundunar sojin Najeriya."

    An danganta Lakurawa da kai hare-hare da dama a al’ummomin arewacin jihar Kebbi da jihar Sokoto dake makwabta.

  13. Matsaloli 7 da suka kamata sufeton ƴansadan Najeriya ya fara magancewa

    ...

    Asalin hoton, Bayo Onanuga/Facebook

    A ranar 25 ga watan Fabrairu ne Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya miƙa wa sabon muƙaddashin babban sufeto janar na ƴansandan ƙasar Olatunji Rilwan Disu takardar fara aiki.

    Tuni sabodan shugaban ƴansandan ya karɓi tutar fara aiki daga tsohon sufeto janar na ƴansandan ƙasar Kayode Egbetokun wanda ya ajiye aiki bisa wasu dalilai, ciki har da wasu abubuwa da suka danganci "iyali."

    A watan Yunin 2023 ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naɗa Kayode Egbetokun a matsayin sufeta-janar na ƴansandan ƙasar.

    Jim kaɗan bayan naɗa shi lokacin ritayarsa ta yi, amma Tinubu ya ƙara masa shekara huɗu, da nufin zai yi aiki zuwa watan Yunin 2027, amma sai kwatsam ya ajiye aiki.

    Ganin shugaban na ƴansanda ya karɓi aiki a daidai lokacin da ƙasar ke fuskantar matsalolin tsaro daban-daban, sai wasu suke ganin tamkar ba dole ba ne a samu wani gagarumin sauyi.

    Wannan ya sa muka yi tankaɗe da rairaya domin zaƙulo wasu muhimman abubuwa da suka kamata saboda sufeto janar ɗin ya fara mayar da hankali a kansu domin fara aiki da ƙafar dama.

  14. An zargi RSF da kashe tare da cin zarafin naƙasassu yayin ƙwace El Fasher a Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Human Rights Watch ta zargi dakarun ƙungiyar RSF da kai wa mutane masu lalurar nakasa hari tare da cin zarafinsu da kuma kashesu a lokacin da suka ƙwace birnin El fasher a yankin Darfur a watan octoban daya gabata.

    A cikin wani sabon rahoto da ta fitar, ƙungiyar ta ce mayaƙan RSF sun riƙa neman mutane masu nakasa da kuma tabin hankali.

    Ƙungiyar human rights watch ta yi magana da mutum 22 da suka tsira da kuma shaidu inda ta tattara bayanai akan waɗanda aka kashe da waɗanda aka yi wa duka ko aka tsare ba tare da sun aikata wani laifi ba

    Waɗanda suka tsira sun faɗawa ƙungiyar cewa da dama daga cikin waɗanda suka rasa gaɓɓoɓinsu mayakan RSf sun daukesu a matsayin sojojin Sudan kuma an kashesu.

    Kawo yanzu kungiyar RSF ba ta ce komai kan zargin

  15. Tinubu ya tsawaita hana fitar da ƙwallon kaɗanya zuwa ƙasashen waje

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tsawaita hana fitar da ɗanyen ƙwallayen kaɗanya zuwa ƙasashen waje da tsawon shekara ɗaya, daga 26 ga Fabrairu 2026 zuwa 25 ga Fabrairu 2027.

    Mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce matakin na nuna ƙudirin gwamnati wajen bunƙasa masana’antu da ƙara darajar kayayyakin cikin gida, da kuma cimma manufofin shirin sabunta fata.

    Sanarwar ta ce manufar tsawaita haramcin ita ce ƙarfafa sarrafa ƙwallon kaɗanya a cikin ƙasa da inganta rayuwar al’ummomin da ke noma ta.

    Domin tabbatar da aiwatar da shirin yadda ya kamata, shugaban ƙasar ya ba da umarni ga ma’aikatu da hukumomi su haɗa kai wajen samar da tsari na ƙasa da zai daidaita manufofin masana’antu da kasuwanci da zuba jari a dukkan sassan harkar kaɗanya.

    Gwamnatin tarayya ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da ke tallafa wa masana’antu na cikin gid tare da samar da ayyukan yi da ƙarfafa matsayin Najeriya a kasuwar kayayyakin noma ta duniya.

  16. An kama ko tsare ’yan jarida 44 a Habasha a shekarar 2025 - Rahoto

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani sabon rahoto da ƙungiyar tallafa wa kafafen yaɗa labarai ta Duniya IMS ta fitar ya nuna cewa aƙalla ’yan jarida 44 ne aka sace ko aka tsare a Habasha a shekarar 2025.

    Rahoton ya bayyana cewa an samu ƙaruwar kai wa ƴan jarida hare-hare, da kamun ba gaira ba dalili, da kuma barazanar kuɗi ga ’yan jarida da gidajen watsa labarai.

    Binciken ya nuna cewa matsin lamba kan kafafen yaɗa labarai ya ci gaba kamar yadda aka gani a 2024, lokacin da aka daure ’yan jarida 43.

    Kungiyar ta bayyana shekarar 2025 a matsayin lokaci mai matuƙar damuwa ga ’yan jaridar ƙasar, sakamakon yawaitar tsare-tsare da sace-sace da muzgunawa da suke fuskanta.

    Rahoton ya kuma bayyana irin haɗurran da sassa daban-daban na kafafen watsa labarai ke fuskanta yayin da suke aiki a yanayi mai ƙara zama haɗari, wanda matsalolin siyasa da dokoki da tsaro, da tattalin arziki ke haddasawa.

  17. Gwamnatin Jigawa za ta karɓi Walida daga hannun DSS

    ...

    Asalin hoton, Umar Namadi/FB

    A yau ne ake sa ran gwamnatin jihar Jigawa za ta karɓi Walida Abdulhadi ƴar asalin jihar, wadda ake zargin wani jami'in DSS ya sace ta tare da sauya mata addini daga hannun hukumar DSS.

    Wannan na zuwa ne bayan cimma matsaya a tattaunawar ƙarshe da aka gudanar cikin dare tsakanin hukumomin da abin ya shafa.

    Sakataren yaɗa labaran gwamnatin jihar, Hamisu Muhammad Gumel, ya shaida wa BBC cewa DSS ta amince da miƙa yarinyar a daren Laraba ga gwamnatin jihar dalilin da ya saka Walida ta saka kwana a hannun DSS har zuwa lokacin da gwamnan jihar zai karɓe ta a hukumance.

    A cewarsa, “an amince cewa gwamnatin Jigawa za ta karɓe ta a yau Alhamis."

    Ya ce "mataki na farko bayan karɓar Walida shi ne kai ta asibiti domin a duba lafiyarta, sannan daga baya a tsara yadda za a haɗa ta da iyayenta tare da ɗaukar sauran matakan kulawa da suka dace."

    Lamarin Walida ya jawo hankalin jama’a a faɗin ƙasar, inda ƙungiyoyin farar hula ke ta kira da a yi mata adalci.

    Tun da farko an zargi wani jami’in DSS da sace ta daga Jigawa tare da tilasta mata aure har ta haihu da kuma sauya mata addini.

    A watan da ya gabata ne wata kotu ta bayar da umarnin a sake ta a haɗa ta da iyayenta, umarni da ake ganin matakin yau na karɓarta zai tabbatar da aiwatar da shi.

  18. An zargi Amurka da hana gwamnatin Venezuela biyan kuɗin kare Maduro a kotu

    ....

    Asalin hoton, AFP

    Lauyan hamɓararran shugaban Venezuela, Nicolas Maduro, ya zargi mahukuntan Amurka da toshe duk wata hanya da gwamnatin Venezuela zata biya kuɗaɗen shari'a ga wanda ya ke karewa.

    Ana dai tsare da Maduro da mai ɗakinsa ne a wani gidan yari da ke New York bisa laifin safarar miyagun ƙwayoyi.

    Cikin wata wasiƙa da ya rubutawa kotu, lauyan Barry Pollack, ya ce tun da farko baitul malin ƙasar ta amince da biyan kuɗaɗen amma daga bisani sai ta janye ba tare da wani bayani ba.

    Ya ce rashin bayar da dama a biya kudaden ya sabawa dokokin shari'a. Mr Maduro da mai dakinsa sun musanta tuhume tuhumen da ake musu.

  19. Tinubu ya buƙaci majalisa ta gyara ƙundin mulki domin kafa ‘yansandan jihohi

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/X

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci shugabannin Majalisar Dattawa su fara nazarin yiwuwar gyaran ƙundin tsarin mulki domin samar da dokar da za ta ba da damar kafa ‘yansandan jihohi, a wani yunkuri na magance matsalolin rashin tsaro da ke addabar ƙasar.

    Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne yayin wata walimar buɗe baki da ya shirya wa sanatoci a fadar shugaban ƙasa, inda ya ce "lokaci ya yi da za a bai wa jihohi ƙarin iko wajen kula da tsaron yankunansu."

    Ya ce "kafa ‘yan sandan jihohi zai taimaka wajen daƙile ayyukan ta’addanci da garkuwa da mutane, da hare-haren ‘yan bindiga, tare da ƙarfafa tattara bayanan sirri da kuma saurin mayar da martani idan barazana ta taso a cikin al’umma."

    Tinubu ya jaddada cewa tsarin rarraba ikon ‘yan sanda zai taimaka wajen haɗa kai tsakanin hukumomin tsaro na tarayya da na jihohi, tare da inganta yadda ake gudanar da ayyukan tsaro bisa sahihan bayanai.

    Ya kuma ce duk da kalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnati na da ƙudurin ganin an samar da mafita mai dorewa.

    A nasa bangaren, shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa sun ƙara yawan kuɗaɗen shiga ga jihohi, abin da ya ce zai taimaka wajen samar da muhimman ababen more rayuwa da bunkasa ci gaba a fadin ƙasar.

    ....

    Asalin hoton, Bayo Onanauga/X

  20. Yau za a tantance yiwuwar cimma yarjejeniyar nukiliya tsakanin Amurka da Iran

    ...

    Asalin hoton, Reuters/ EPA

    A yau ne za a gudanar da zagaye na uku na tattaunawar da ake yi tsakanin Amurka da Iran a Geneva kan shirin makamin nukiliyar Tehran.

    Tattaunawar za ta tantance ko za a iya cimma wata yarjejeniya, inda Iran za ta iya haƙura da wasu daga cikin buƙatunta kan shirinta na nukiliya, ciki har da wasu ɓangarorin shirinta na Uranium.

    Ana kallon wannan tattaunawar da matukar muhimmanci, musamman yayin da Amurka ke ƙara karfin dakarunta a Gabas ta Tsakiya, mafi yawa tun bayan mamayar da ta kai wa Iraƙi a shekarar 2003.

    Iran itama ta ƙara karfafa shirinta domin tunkarar duk wani hari da ka iya zuwa.

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan batun nukiliya, amma ya jaddada cewa yadda Iran ke dagewa kan cire batun makamai masu linzami shi ne babban ƙalubale a tattaunawar.