EndSars: Hotunan yadda aka gudanar da zanga-zangar a Najeriya

An kwashe fiye da mako biyu ana zanga-zanga kan cin zarafin da rundunar 'yan sandan SARS, wadda aka rusa, ta rika yi wa 'yan Najeriya.

Asalin hoton, Reuters

Asalin hoton, EPA

Lamarin ya soma ne sakamakon zargin da 'yan Najeriya ke yi wa rundunar SARS wajen daure mutane ba bisa ka'ida ba, da cin zalinsu da kuma kashe su, abin da ya kai ga rusa ta.

Shugaba Buhari ya rusa rundunar ranar 11 Oktoba.

Asalin hoton, EPA

Tun daga lokacin, masu zanga-zangar sun yi ta kira kan kawo sauyi ga tsarin tsaron kasar da kuma yadda suke ganin za a kawo sauyi ga kasar baki daya.

Asalin hoton, Reuters

Asalin hoton, EPA

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Wani gini kusa da Lekki-Ikoyi Toll Gate da ke Lagos ranar 21 ga watan Oktoba

Ganau sun ce an kashe akalla mutum 12 sannan aka jikkata mutane da dama lokacin da sojoji suka bude wuta kan masu zanga-zanga.

Kungiyar Amnesty International ta ce ta "samu bayanai masu kwari" kan kashe-kashen da aka yi.

Gwamnan jihar ya ce babu wanda ya mutu, ko da yake mutum 25 aka jikkata.

A London, masu zanga-zangar sun kwashe kwanaki suna fitowa kan tituna.

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, Joseph Okpako

An gudanar da zanga-zanga a wajen ofisoshin jakdancin Najeriya da ke kasashe da dama, ciki har da Nairobi, Kenya (a hoton da ke kasa)...

Asalin hoton, Getty Images

...da kuma ofishin jakadancin Najeriya da ke Pretoria, Afirka ta Kudu (hoton da ke kasa).

Asalin hoton, PHILL MAGAKOE

Asalin hoton, Getty Images

.