Satar garin tuwo ta tilasta ba da katin shaida a wurin niƙa a Kano
A baya da wuya ka ji an ce an sace garin tuwo a wurin niƙa duk da cewa a kan samu yanayin da ake yin musaya, wato wani ya ɗauki na wani amma ya bar nasa bisa kuskure.
To amma a yanzu mazauna wasu unguwanni a birnin Kano, na ƙorafi dangane da yadda garin tuwonsu ke ɓacewa a wajen niƙa a ƴan kwanakin nan.
Wannan ne dai ya sanya wasu masu inji da ke yin niƙan suka samar da hanyar rage sace-sacen, inda suka fito da bai wa duk wanda ya kai niƙa shaidar hakan.
Wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da wani rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce an samu karin mutum fiye da milyan guda da ke fama da karancin abinci a jihar Kano sakamakon annobar korona.
Har wa yau, wasu na alaƙanta al'amarin da irin matsin rayuwar da jama'a suka samu kansu a ciki saboda tashin gwauron zabi da farashin kayan masarufi ya yi sakamakon karin kudin man fetur da wutar lantarki da gwamnatin Najeriya ta yi.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai