Ebola: Bazuwar da cutar ke daɗa yi na sanya damuwa
Asalin hoton, AFP
Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce ta damu game da ɓarkewar cutar ebola a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo, wadda ta zama mafi yawa da aka taɓa samu a yankin arewa maso yammacin ƙasar.
An ba da rahoto mutum 56 ne suka kamu da cutar a lardin Equateau na Jamhuriyar Kongo tun bayan ɓullarta a watan Yuni.
Daraktar Hukumar Lafiyar a nahiyar Afirka, Dr Matshidiso Moeti ta ce "Wannan babban abin damuwa ne, musammam ma ganin cutar ta zarce yawan da aka taɓa samu a wannan yanki, wanda aka killace shi lokacin mutanen da cutar kama ba su wuce 54 ba.
A cewarta, wasu daga cikin mutanen da suka kamu na zaune ne a can yankuna masu nisa da ke zagaye da dazuka, abin da sanya buƙatar ƙarin ƙwazo da kayan aiki don kai ɗauki.
Jami'ar lafiyar ta ce an koyi darussa a lokacin ɓarkewar cutar cikin wannan yanki baya a shekara ta 2018, lamarin da ya sa aka yi wa mutane sama da dubu goma sha biyu allurar riga-kafi a tsawon mako shida.
A cikin watan Yuni ne, hukumomin lafiya suka ayyana kawo ƙarshen ɓarkewar cutar mafi muni a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo.
Cutar ebola dai ta kashe fiye da mutum dubu biyu da ɗari biyu cikin lardunan arewa maso gabashin ƙasar uku.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai