'Mun gano dalilai 7 na mace-mace a arewacin Najeriya'
Tawagar ƙwararrun da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa yankin arewacin kasar domin bincike sanadiyyar mace-mace a wasu jihohin yankin ta ce ta kasa mace-macen gida bakwai kuma yanzu ta kusa kammala rangadin da take a jihohin, inda daga bisani za ta fitar da bayani.
Shugaban kwamitin Dr Nasiru Sani Gwarzo ya ce kawo yanzu sun ziyarci jihohi shida daga cikin takwas da aka fuskanci mace-macen mutane a watan jiya.
Dr Gwarzo ya kuma sun gano abubuwa da yawa game da mutuwar ta farat ɗaya da mutane suka rinka yi a jihohin arewacin kasar.
"Mun je har makabarta inda muka kidaya kabarbarun mutane wasu mutanen kuma sun yi mana bayanai kan mamatansu. Amma kuma mun gano yadda a wasu jihohi an kambama mace-mace.
Mun samu samfurin mamata a jihohi da dama kuma muna jiran sakamakon abin da ya kashe su."
Shugaba Muhammadu Buhari ne dai ya tura tawaga ta musamman zuwa jihar Kano, inda aka samu karuwar mace-mace irin ta farat daya.
Sakamakon kuma samun irin mace-macen a jihohin Jigawa da Sokoto da Yobe da Borno da dai sauran jihohi arewacin kasar, sai shugaba Buhari ya fadada aikin kwamitin.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai