Ramadan 2019: Musulmi sun fara azumi
Asalin hoton, Getty Images
A Najeriya, mai alfarma sarkin Musulmi, Sultan Sa'ad Abubakar III, wanda shi ne shugaban majalisar koli kan harkokin addinin musulunci ya bayyana ganin watan a garuruwa daban-daban a Najeriya a wani taron manema labarai da aka gudanar a daren Lahadi.
Wannan na zuwa ne bayan ganin jinjirin watan da aka yi a wurare daban-daban a fadin duniya.
Kwamitin ganin wata na Najeriya ya wallafa jawabin sarkin a shafin Twitter inda sarkin ya umarci jama'a da su tashi da azumi ranar Litinin.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Akasarin Musulmai a fadin duniya za su tashi da Azumin watan Ramadan ranar shida ga watan Mayun 2019 wanda hakan ya zo dai-dai da daya ga watan Ramadan 1440.
Sarkin ya yi kira da a yawaita ibada a cikin watan na Ramadan kuma a ci gaba da addu'a ga shugabanni.
Baya ga Najeriya Musulmai a wasu kasashen duniya irin su Saudiyya za su fara azumin na watan Ramadana a ranar Litinin.
Ramadan dai wata ne mai alfarma ga musulmi inda ake matsa kaimi kan ibada da addu'o'i.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai