An yi zanga-zangar adawa da ziyarar Yariman Saudiyya a Tunusiya
Daruruwan 'yan Tunusiya suna zanga-zangar adawa da ziyarar da Yarima mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ke yi a kasar, a yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce ka kisan fitaccen dan jarida Jamal Khashoggi.
Asalin hoton, Getty Images
Masu fafutuka da kuma 'yan jarida sun yi maci a tsakiyar babban birnin kasar tunis, suna ihun cewa Yarima mai jiran gadon Saudiyya mai kisan kai ne kuma ba a maraba da shi a Tunisiya.
Asalin hoton, Getty Images
Wasu majiyoyi na Tunusiya sun ce an kafe wani katon hoton Yariman a ofishin kungiyar 'yan jaridar kasar da ke nuna shi dauke da zarto - wanda ke nufin da shi aka sassara Mista Khashoggi.
Asalin hoton, Getty Images
Yarima Muhammad wanda ya sha yin watsi da zargin hannu a kisan, yana ziyarar ne a kasashen Larabawa, irin ta ta farko da yake yi tun bayan kisan Mista Khashoggi.
Asalin hoton, Getty Images
Asalin hoton, Getty Images
Asalin hoton, Getty Images
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai
{{rankTranslation}}