Ana farautar wanda ya kashe maguna a Saudiyya
Asalin hoton, Twitter
Hukumomin a Saudiyya suna farautar wani mutum wanda ake zargi da kashe maguna da dama a kasar.
An kaddamar da binciken ne bayan wani faifan bidiyo ya bayyana a kafofin sada zumunta wanda yake nuna wani mutum ya harbe wasu maguna a birnin Jeddah.
Hukumomin kasar sun ce suna nemansa ruwa a jallo.
Bidiyon wanda aka wallafa a shafin sada zumunta na Snapchat ya nuna wani mutum rike da bindiga yana bin unguwanni yana kashe maguna.
Hakan ya sa mutane da dama sun bayyana damuwarsu a kafofin sada zumunta, yayin da wasu suka bukaci a binciki al'amarin.
Bidiyon ya nuna daya daga cikin magunan tana shure-shuren mutuwa bayan an harbe ta.
Mutumin wanda ya bayyana a cikin bidiyon amma fuskarsa ta kasance a rufe.
Ba a dai bayyana sunan mutumin ba tukuna. Hakazalika ba a san abin da ya sa shi yin hakan ba.
Ba wannan ba ne karon farko da aka taba samun kashe-kashen mage ba.
Don ko a watan Yuni an sanyawa wadansu maguna 200 guba a abinci a kauyen Saint Pierre la Mer na kasar Faransa.
Hakazalika, a watan Yuli an yanke wa wani mutum a jihar California ta kasar Amurka hukuncin dauri shekara 16 bayan da ya amsa laifin azabtarwa da kuma kisan wasu maguna 18.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai