An dage hawan sallah a Katsina
Fadar masarautar Katsina ta fitar da wata sanarwar, wadda a ciki ta aike sakon jaje ga daukacin jama'arta kan ibtila'in kashe-kashen da mutanen gundumomin Batsari, da Dan-Musa, da Kankara da Wagini da sauransu wuraren da abun ya shafa suka samu kansu a ciki.
Sakataren masarautar Alhaji Bello M IFO shi ne ya fitar da ita, tare da shaida wa jama'a ce wa sakamakon halin da suka samu kansu a ciki na alhini da jimami, masarautar ta yanke shawarar a wannan karon ba za a yi hawan sallah kamar yadda aka saba ba.
Alhaji Bello ya ce Mai-martaba sarkin Katsina Dr Alhaji Abdulmumin Kabir Usman CFR, da majalisar masarautar ne suka ga dacewar dage duk wasu shagulgula don nuna alhini kan abin da ya samu jama'arsu.
A karshen sanarwar ta ce za a je sallar idi kamar yadda aka saba, da yin addu'o'in neman zaman lafiya ga jihar Katsina da Najeriya baki daya.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai