Nigeria: EFFC ta kama mutum 865 a Kaduna
Asalin hoton, EFCC
A Nigeria, ga alamu kokarin da hukumomin kasar ke yi na fadada yaki da cin hanci da rashawa zuwa matakin kasa ya fara tasiri wajen kama wadanda ake tuhuma da almundahana.
Misali a jihar Kaduna kadai, hukumar yaki da cin hanci da karbar rashawa ta EFCC ta ce ta kama mutum fiye da 860 da ake tuhuma da hannu a almundahana cikin 'yan watanni da bude ofishinta a can.
A cikin wata sanarwa, Shugaban Hukumar a shiyyar Kaduna, Ibrahim Baffa, ya ce an kakkama mutanen ne sakamakon koke-koke har 220 da aka shigar gaban hukumar tasa kan wadannan mutanen.
Ya ce kawo yanzu sun fara bincike kan koke-koke 130 daga cikinsu inda har suka shigar da kara kan koke-koke guda 10 a gaban kotu.
Ofishin inji sanarwar, ya samu kwato Naira miliyan 227 daga hannun wadannan mutanen cikin har da dalar Amurka dubu 17.
Da ma dai masu fafutukar yaki da almundahana a kasar sun jima suna shawarartar hukumomi da su ba za komarsu zuwa kasa domin ko can ma ana tafka ta'asa.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai