Gasar La Liga za ta ci gaba da gudana ko ba Messi
Asalin hoton, Getty Images
Shugaban gasar La Liga, Javier Tebas ya ce a shirye yake idan Messi zai bar Spaniya - ya kuma soki Manchester City da ake sa ran za ta sayi dan kwallon.
Messi ya bukaci izinin barin Barcelona a cikin watan Agusta - kungiyar da ya je yana da shekara 13 daga baya batun ya lafa, bayan da aka tsawaita yarjejeniyar zamansa a Camp Nou.
Kyaftin din tawagar Argentina ya samu rashin jituwa da Josep Bartomeu - wanda ya ajiye aikin shugabantar Barcelona a cikin watan Oktoba.
Shi dai Tebas na son Messi ya ci gaba da taka leda a Spaniya, amma ya ce ko ba dan kwallon za a ci gaba da gudanar da wasannin.
Shugaban La Liga ya ce Neymar ya bar Spaniya a 2017 daga Barcelona zuwa Paris St Germain, kuma a 2018 Cristiano Ronaldo ya bar Real Madrid zuwa Juventus an kuma ci gaba da buga gasar.
Messi mai shekara 33, yarjejeniyarsa zai kare a karshen kakar bana, daga nan kowace kungiya za ta iya daukar sa.
Tebas ya yi nuni da cewar watakila Messi ya koma buga gasar Premier League a filin wasa na Etihad - koda yake wata majiya ta ce babu wani daga mahukuntan Manchester City da ya yi magana kan sayo Messi.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai