UAE ta dakatar da jigilar mai a matatar Fujairah
Kamfanin man fetur na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ya dakatar da jigilar mai a matatarsa da ke Fujairah bayan harin jirgi mara matuƙi da Iran ta kai.
Matatar dai tana kusa ne da hanyar shiga mashigar Hormuz. Tun da farko, jirgi mara matuƙi da aka harba a filin jirgin Dubai ya janyo tsaiko a sufurin jirgin sama.
Ita ma dai Iran ta ce ta kai wasu hare-hare a birane uku mafiya girma a Iran, sannan ta ce ta tarwatsa wani gida a Tehran da ake amfani da shi wajen kitsa hare-hare.
Ita dai Amurka ta nace cewa babban burinta shi ne daƙile barazanar makaman Iran masu linzami da jirage marasa matuƙa da sojin ruwa da kuma hana ƙasar ƙera su.