Kocin Iraqi ya buƙaci a ɗage wasan cike-gurbin kofin duniya saboda yaƙin Iran

Asalin hoton, Getty Images
Kocin Iraqi Graham Arnold ya yi kira a ɗage wasan cike-gurbi da tawagar ƙasar za ta fafata a ƙarshen wannan watan zuwa wani lokacin daban saboda yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi a Iran.
Tawagar ƙwallon ƙafa ta Iraqi za ta fafata ne ko dai tawagar Bolivia ko kuma ta Suriname a birnin Monterrey da ke Mexico a ranar 31 ga Maris.
Wanda ya samu nasara a wasannin ne zai samu gurbi a gasar cin kofin duniya ta shekarar 2026 da za a buga a ƙasashen Amurka da Mexico da Canada da za a fara daga ranar 11 ga watan Yuni.
Sai dai Iraqi na fargabar ba za ta iya tafiya zuwa ƙasar da za a buga wasan ba a Mexico saboda yanayin yanayin yaƙin ya kawo ƙalubale kan zirga-zirgan jiragen sama a Gabas ta Tsakiya.
Tun ranar 28 ga watan Fabrairu da aka ƙaddamar da hare-hare a Iran ne aka rufe sararin samaniyar Iraqi domin tsaro.


















