Trump ya ce an kashe jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa an kashe jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.
A cikin saƙon, Trump ya ce "wannan adalci ne ba ga al'ummar Iran kawai ba, har da Amurkawa, da kuma al'ummar ƙasashen duniya waɗanda Khamenei da ƴan korensa suka kashe ko suka azbtar.
"Ya gaza zulle wa bayanan sirrinmu da kuma fasaharmu ta bibiya, tare da aiki kafaɗa da kafaɗa da Isra'ila, yanzu babu shi, ko sauran jagororin da ak kashe tare da shi.
"Wannan ce babbar dama ga al'ummar Iran su sake karɓe iko da ƙasarsu.
"Amma gagarumin luguden wuta na ɗauki ɗaiɗai zai ci gaba, ba tare da ƙaƙƙautawa ba a tsawon mako ko kuma har zuwa lokacin da ya kamata domin cimma manufarmu ta zaman lafiya a faɗin Gabas ta Tsakiya da duniya baki ɗaya."














