Iran ta ci gaba da kai hare-hare kan Isra'ila ta yankin Gulf

Asalin hoton, ..
Iran ta ci gaba da kai hare-hare kan Isra'ila da sauran ƙasashen yankin Gulf.
A Kuwait babban kamfanin na ƙasar ya ce an kai wa matatar mai ta Mina al- Ahmadi hari da jirage marasa matuƙa, yayin da ma'aikatan agaji ke ƙoƙarin kashe gobarar da ta tashi bayan hare-haren.
Can a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa hukumomin ƙasar sun bayar da rahoton kai hare-hare.
A Isra'ila sojojin ƙasar sun ce na'urorin tsaron samniyarta na aikin kakkaɓo makaman linzami da Iran ta harba cikin ƙasar.



