'Islamabad na shirin karɓar baƙuncin tattaunawar Amurka da Iran karo na biyu'

Asalin hoton, Reuters
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya bayar da rahoton tsaurara matakan tsaro a Islamabad, babban birnin Pakistan.
Yayin da jami'an Amurka da na Iran ke shirin ci gaba da tattauna batutuwan da suka sha bamban don kawo ƙarshen yaƙin Iran.
Kawo yanzu dai ba a bayyana wuri da lokacin da za a gudanarwa da tattaunawar ba.
Mashigar Hormuz - wadda ke cikin batutuwan da ɓangarorin biyu suka yi saɓani - ta kasance a rufe, saboda ci gaba da datse tasoshin ruwan Iran da Amurka ke yi.
Iran ta ce jiragen ruwa za su wuce ta mashigar ne kawai bisa amincewar dakarun IRGC.
Duka ɓangarorin biyu dai sun ɗauki tsauraran matsayi game da batun.
Shugaba Trump ya jaddada cewa Amurka za ta bari jiragen Iran su shiga ko fita daga tasoshin ruwanta ne kawai idan aka cimma yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin, yayin da Iran ta zargi Amurka da rashin mutunta yarjejeniyar wucin gadi da aka cimma.




