Amurka da Iran sun sanar da tsagaita wuta na tsawon mako biyu, bayan da shugaban Amurka, Donald Trump, ya janye barazanar kai wani gagarumin hari kan Iran, jim kaɗan kafin cikar wa’adin da ya bayar.
Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya tabbatar da cewa za su buɗe mashigar Hormuz domin jiragen ruwa su riƙa wucewa a lokacin tsagaita wutar, amma da rakiya daga sojojin Iran.
Rahotanni sun nuna cewa an cimma yarjejeniyar ne mintuna goma kafin cikar wa’adin da Trump ya bayar na kai hare-hare.
An kulla yarjejeniyar da ƙarfe 6:30 na yamma agogon Washington, wanda ya yi daidai da ƙarfe 11:30 na dare a agogon Najeriya.
Firaministan Pakistan ya sanar da fara aiki da yarjejeniyar nan take, inda yayi maraba da matakin tare da gayyatar dukkan ɓangarorin da su hallara a wani babban taro a Islamabad ranar Juma’a 10 ga watan Afrilu, domin ci gaba da tattaunawa da nufin samun fahimtar juna.
Daga cikin buƙatun da Iran ta gabatar akwai tabbacin cewa ba za a sake kai mata hari ba, za ta ci gaba da kula da mashigar Hormuz, da kuma ci gaba da sarrafa makamashin uranium da take da shi. Haka kuma ta buƙaci a ɗage takunkuman da aka ƙaƙaba mata.
Sauran buƙatun sun haɗa da dakatar da wasu yarjejeniyoyi da suka shafi Majalisar Tsaron Majalisar Ɗinkin Duniya da Hukumar Kula da Makamashin Atomic ta Duniya da biyan diyya da janye sojojin Amurka daga yankin Gabas ta Tsakiya, da kuma dakatar da dukkan hare-hare ciki har da na Lebanon.
A nata ɓangaren, Amurka ta amince da tsagaita wutar ne da sharadin cewa jiragen ruwa za su rika wucewa ta mashigar Hormuz ba tare da wata barazana daga Iran ba.
Isra’ila ma ta goyi bayan matakin na tsagaita wutar, bayan da Iran ta amince da buɗe mashigar Hormuz da kuma dakatar da hare-hare kan Amurka, Isra’ila da ƙasashen yankin Gulf.
Sai dai har yanzu akwai ƙarancin yarda da juna tsakanin Amurka da Iran, a daidai lokacin da ake shirin ci gaba da tattaunawa. A baya, sau biyu kasashen biyu sun fara irin wannan tattaunawa, amma rikici ya kan ɓarke kafin a kai ga cimma matsaya.