Ana ci gaba da musayar wuta tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka
Rahotanni sun ce an sake yi wa Iran ruwan bama-bamai, inda rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kammala abin da ta kira wasu jerin hare-hare ta sama a kan wuraren da ta ce na gwamnatin Iran din ne, a babban birnin ƙasar, Tehran.
A cikin dare rundunar sojin Amurka ta fittar da wani bidiyo da ke nuna sojojinta na jefa abin da ta kira bama-bamai na yankan-shakku a wuraren da ta ce na soji ne da ke karkashin kasa.
Kamar dai yadda aka saba, ita ma Iran din ba ta sarara ba a martanin da take kai wa, inda jamiai a Kuwait suka ce wuta ta tashi a babban filin jirgin sama na kasar, sakamakon harin jirgin sama maras matuki da Iran ta kai a kan wasu tankunan mai.
Can a Bahrain Iran din ta kai hare-hare cikin dare inda gobara ta tashi .
Haka kuma hukumar jamian tsaro na teku ta Birtaniya ta ce wani makami mai linzami ya fada kan wani jirgin ruwa na dakon mai a gabar tekun Qatar