Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 16/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 16/01/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi, Aisha Babangida da Abdullahi Diginza

  1. Ana ci gaba da ƙirga ƙuri'u a zaɓen Uganda

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana ci gaba da ƙidayar ƙuri'u a ƙasar Uganda, bayan da aka gudanar da zaɓen da ya fuskanci tsaiko sakamakon tangarɗar na'urori.

    Shugaban ƙasar mai ci Yoweri Museveni da ke neman wa'adi na bakwai bayan shafe shekaru arba'in yana mulki, ya zuwa yanzu ya samu fiye da kashi 74 cikin 100 na ƙuri'un da aka ƙirga.

    Babban abokin hamayyarsa fitaccen mawaƙi Robert Kyagulanyi wanda aka fi sani da Bobi Wine na biye masa inda ya samu kusan kashi 20 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa.

    Tuni dai jam'iyyar Wine ta National Unity Platform (NUP) ta nuna shakku kan sahihancin sakamakon.

    NUP ta kuma ce an yi wa Bobi Wine ɗaurin talala, inda jami'an tsaro suka kewaye gidansa da ke Kampala.

    A gefe guda kuma, wani ɗan majalisar adawa ya zargi jami'an tsaro da kashe mutane goma a gidansa da ke tsakiyar ƙasar Uganda.

    Ƴan sanda dai sun musanta wannan iƙirarin, suna masu cewa jami'an na mayar da martani ne kan wani yunƙurin kai hari a wata cibiyar zaɓe.

    Tun da farko, Bobi Wine ya buƙaci magoya bayansa da su yi zanga-zanga idan an sace ƙuri'un.

    Yayin da aka kidaya fiye da rabin ƙuri’un da aka kaɗa, hukumar zaɓen ƙasar ta ce tana sa ran bayyana wanda ya lashe zaɓen a ƙarshen ranar Asabar.

  2. Jagoran adawa ya buƙaci a taimaka wurin hambarar da gwamnatin Iran

    Reza Pahlavi

    Asalin hoton, Reuters

    Ɗan marigayi Shah (sarkin Iran) da ke gudun hijira ya yi kira ga duniya da su taimaka wa masu zanga-zangar hambarar da gwamnatin Iran, yana mai cewa yana da yaƘinin "Jamhuriyar Musulunci za ta faɗi nan bada jimawa ba".

    Reza Pahlavi, jagoran ƴan adawa da ke Amurka, ya yi kira da a kai hare-hare kan dakarun kare juyin juya halin Iran wanda ya ce "zai sauƙaƙa ayyukanmu da kuma hana ƙarin asarar rayuka".

    Sama da masu zanga-zanga 2,000 ne aka kashe a cewar ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama, a zanga-zangar da ta fara kan tattalin arzikin ƙasar a ranar 28 ga watan Disamba da ta rikiɗe zuwa kiraye-kirayen kawo ƙarshen mulkin shugaban addinin Iran Ali Khamenei.

    Gwamnatin Iran ta kira zanga-zangar da tashe tashen hankula da maƙiyan Iran ke marawa baya.

    Pahlavi dai ya bayyana a matsayin wani jigo a cikin ƴan adawar ƙasar Iran, kuma a baya ya buƙaci Iraniyawa da su ƙara zafafa zanga-zangar.

    Sai dai hukumomi sun tunkari masu zanga-zangar da munanan mataikai, wanda ya haɗa da rufe intanet da sauran kafafen sadarwa.

  3. Canada da China sun cimma wata gagarumar yarjejeniyar kasuwanci

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    China da Canada sun sanar da cimma wata yarjejeniyar kasuwanci, bayan wata muhimmiyar tattaunawa da suka yi a Beijing.

    Firaministan Canada Mark Carney, ya ce yarjejeniyar, wadda ta biyo bayan shekaru da dama ana samun tsamin dangantaka, za ta rage haraji a fannoni da dama, da suka haɗa da motoci masu amfani da lantarki, tare da barin ƴan Canada shiga China ba tare da biza ba.

    Shugaba Xi Jinping ya jinjinawa yarjejeniyar, inda ya jaddada cewa akwai buƙatar ɓangarorin biyu su martaba ƴanci da mutuncin junan su.

    Da yake magana da ƴan jarida, Mista Carney ya ce duniya ta sauya sosai, inda ya bayyana China a matsyin abokiyar kasuwanci mai mutunci.

  4. Ambaliya ta kashe mutum 19 a Afrika ta kudu

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Ambaliyar ruwa a lardunan Limpopo da Mpumalanga da ke arewacin Afirka ta Kudu ta tilastawa shahararren gandun dajin Kruger dakatar da ziyara tare da kwashe wasu baƙi da ma'aikatansu ta jirgin sama mai saukar ungulu.

    Aƙalla mutane 19 ne suka mutu a ƴan makonnin nan a ƙasar Afirka ta Kudu bayan da ruwan sama kamar da bakin ƙwarya ya haddasa ambaliyar ruwa da ta lalata dubban gidaje, tare da share wasu gidaje baki ɗaya.

    Daga cikin waɗanda bala'in ya shafa har da wani yaro ɗan shekara biyar a garin Giyani da ke Limpopo.

    Shugaba Cyril Ramaphosa ya gana da iyalan yaron domin jajanta musu yayin da ya ziyarci yankin domin tantance irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

    Hukumar kula da yanayi ta Afirka ta Kudu ta yi hasashen ƙarin ruwan sama a yankunan da abin ya shafa tare da gargaɗin al'ummomin da su kasance cikin shiri.

    A cikin ƴan kwanakin nan an tura jirage masu saukar ungulu da sojoji domin ceto mutane a wasu yankunan da lamarin ya fi shafa.

    Ana kuma tattaro sojoji domin su taimaka wajen sake gina titunan da suka lalace a lardin Limpopo.

    Yawancin makarantu da asibitocin kiwon lafiya sun lalace ko kuma ba za a iya kai wa garesu ba, in ji jami’an yankin.

  5. Trump ya yi barazanar sanya haraji kan ƙasashen da ke adawa da karɓe iko da Greenland

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar sanya haraji kan ƙasashen da ba su amince da yunƙurinsa na neman mamaye yankin Greenland ba.

    A wani taron fadar White House ya bayyana cewa "zai iya sanya haraji kan ƙasashe idan ba su da Greenlanamince da batun karɓe Greenland ba."

    Greenland dai yanki ne mai cin gashin kansa wanda Denmark ke iko da shi.

    Sai dai bai bayyana ƙasashen da za a ƙaƙabawa sabbin harajin ba.

    Denmark da Greenland, da wasu ƙasashe suna adawa da burin na Trump, kuma da yawa a Amurka sun nuna shakku game da wannan batu.

    A yayin da Trump ke magana, wata tawaga ta ƴan majalisar wakilai daga jam'iyyun republican da Democrat ta ziyarci Greenland domin nuna goyon baya ga yankin.

    Tawagar mai mambobi 11 ta haɗa da ƴan jam'iyyar Republican waɗanda suka bayyana damuwarsu game da yunkurin da shugaban ƙasar ke yi mallakar Greenland ko ta halin ƙaƙa saboda dalilan tsaron ƙasa.

    Sun gana da ƴan majalisar dokoki da kuma Firaministan Denmark Mette Frederiksen da takwaranta na Greenland Jens-Frederik Nielsen.

  6. Gwamnatin Myanmar ta soma kare kanta a kotun ICJ

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Myanmar ta soma kare kanta kan tuhume tuhumen da ake yi mata na yin ƙisan ƙare dangi a gaban Kotun duniya ICJ.

    Wakilin Myanmar a Kotun da ke Hague, ya yi iƙirarin cewa ana ƙoƙarin shafa ma ƙasarsa baƙin fenti ne.

    Ƙasar The Gambia ce ta shigar da ƙarar, inda ta zargi gwamnatin Myanmar da saɓaa yarjeniyar Majalisar dinkin duniya kan hana kisan kiyashi a lokacin wani harin soji kan alummar Rohingya a jihar Rakhine a 2017.

    Wakiliyar BBC ta ce Myanmar ta bayyana ayyukan da ta yi a wurin a 2017 a matsayin na yaƙi da ta'addanci, ba wai zalunci ba.

  7. An yi arangama tsakanin jami'an tsaro da ƴan jam'iyyar adawa a Uganda

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Ana samun rahotannin artabu tsakanin ƴan sanda da magoya bayan ƴan jam'iyyar adawa a Uganda, bayan zaɓen shugaban ƙasa da aka yi a jiya Alhamis.

    Kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun ce an hallaka mutane da dama.

    An yi ta samun fargaba bayan da jam'iyyar ɗan takarar shugabancin ƙasar Bobi Wine ta ce jami'an tsaro sun zagaye gidansa a yayin da ake ƙirga ƙuri'u.

    Jam'iyyarsa ta ce jami'an tsaro sun yi mishi ɗaurin talala shi da uwargidansa.

    Wakiliyar BBC ta ce a shafinsa na sada zumunta, Bobi Wine ya yi kira ga magoya bayansa su fita kan tituna su yi zanga zanga.

    Hukumar zaɓen ƙasar ta ce sakamokon farko ya nuna Shugaba Yoweri Museveni na da kashi saba'in da shida na ƙuri'un, yayin da Bobi Wine ke da kaso ashirin.

  8. Man City ta amince da yarjejeniyar fam miliyan 20 don siyan Marc Guehi

    Marc Guehi

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester City ta amince da yarjejeniyar siyan kyaftin ɗin Crystal Palace Marc Guehi a wannan watan kan farashin fam miliyan 20.

    City ta fara tattaunawa da ɗan wasan bayan Ingila, mai shekara 25, a wannan watan sakamakon raunin da ƴan wasan baya Josko Gvardiol da Ruben Dias suka yi.

    Guehi, wanda ake dangantashi da wasu manyan ƙungiyoyin Turai, kwantiraginsa ya kare a bazara mai zuwa, kuma sauran ƙiris ya koma Liverpool a bazarar da ta gabata.

    BBC Sport ta ruwaito a farkon wannan watan cewa City na neman Guehi kuma tattaunawa ta wani mataki cikin sa'o'i 24 da suka gabata.

    Yanzu ana sa ran Guehi zai koma City kan kwantiragin dogon zango a wannan watan.

    Ba a kammala amincewa da sharuɗɗan skwantiragin daga ɓangaren ɗanwasan ba amma ba a tsammanin za su zama matsala.

    City ta riga ta sayi Antoine Semenyo daga Bournemouth a kasuwar musayar ƴan wasa da ake yi a yanzu kan fam miliyan 62.5.

    Batun tafiyar Guehi ya samo asali bayan da kocin Palace Oliver Glasner ya tabbatar da cewa zai bar ƙungiyar idan kwantiraginsa ya ƙare a watan Yuni.

  9. Afrika ta kudu za ta yi bincike kan shigar Iran atisayen sojojin ƙasashen BRICS

    ...

    Asalin hoton, Bloomberg/Getty Images

    Ma'aikatar tsaron Afirka ta Kudu ta ce ta ƙaddamar da bincike kan shigar Iran wani atisayen sojin ruwa na ƙungiyar BRICS da ake yi a cikin makon nan a tekun ƙasar.

    Hakan na zuwa ne bayan Amurka ta zargi ministan tsaron Afirka ta Kudu da sojojin ƙasar da ƙin biyan buƙatar Amurka na cire Iran daga atisayen.

    A cikin wata sanarwa, ma'aikatar tsaron ta ce binciken zai tabbatar da ko an samu rashin fahimta ne ko kuma an yi watsi ne da umurnin da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya bayar kan shigar Iran.

    Afirka ta kudu na ƙarɓar baƙuncin ƙasashen ƙungiyar BRICS ciki har da China da Rasha domin yin atisayen, wanda ake sa ran kammalawa a yau Juma'a.

  10. Yoweri Museveni na kan gaba a sakamakon farko na zaɓen Uganda

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni daga hukumar zaɓe ta Uganda sun nuna cewa shugaban ƙasar, Yoweri Museveni, na kan gaba a sakamakon farko na zaɓen ƙasar.

    Ƙididdigar ƙuri’u ta farko ta nuna Museveni na da kusan kashi 76 cikin 100 na ƙuri’un da aka ƙirga daga kusan kashi 45 na rumfunan zaɓe.

    Babban abokin hamayyarsa, Bobi Wine, na da kusan kashi 20 cikin 100, yayin da sauran ‘yan takara shida suka raba saura.

    Sai dai an samu zarge-zargen maguɗin zaɓe daga Bobi Wine, duk da cewa ba a gabatar da hujja ba.

    Jam’iyyarsa kuma ta ce an tsare shi a gida, inda ya kira magoya bayansa da su fito zanga-zanga.

    Shugaba Museveni mai shekaru 81 na neman wa’adi na bakwai a mulki.

    A halin yanzu kuma, An katse intanet baki ɗaya a ƙasar, yayin da Majalisar Dinkin Duniya ta riga ta yi gargadin cewa zaɓen zai fuskanci tsangwama da danniya.

  11. Shettima ya tafi babban taron tattalin arziki na duniya a Switzerland

    Kashim Shettima

    Asalin hoton, Stanley Nkwocha/X

    Bayanan hoto, Kafin nan Shettima zai ya da zango a Guinea-Conakry

    Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bar Abuja domin halartar babban taron tattalin arziki na duniya karo na 56 da ake gudanarwa a kowace shekara a Davos, ƙasar Switzerland.

    Kafin halartar babban taron, Shettima zai fara da wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da sabon Shugaban Ƙasar Guinea-Conakry, Mamadi Doumbouya, bayan nasarar da ya samu a zaɓe.

    An shirya bikin rantsarwar ne a ranar Asabar, 17 ga Janairu, a filin wasa na GLC Stadium da ke Nongo, a birnin Conakry.

    Halartar mataimakin shugaban ƙasar a bikin rantsarwar na da muhimmanci wajen ƙarfafa jagorancin Najeriya a yankin, da bunƙasa haɗin gwiwar tattalin arziki bisa manufar Tinubu na sabunta fata.

    Wannan mataki na cikin rawar da Najeriya ke takawa a matsayin jagaba a ƙungiyar ECOWAS, musamman wajen tallafa wa Guinea domin komawa kan tafarkin mulkin farar hula bayan shafe shekaru huɗu tana ƙarƙashin mulkin riƙon ƙwarya.

    Kashim Shettima

    Asalin hoton, Stanley Nkwocha/X

    Daga Guinea, mataimakin shugaban ƙasar zai wuce zuwa Davos-Klosters a Switzerland domin halartar babban taron tattalin arziki na duniya, wanda za a gudanar daga ranar 19 zuwa 23 ga Janairu, 2026.

    A yayin taron na Davos, Shettima zai gana da shugabannin duniya da masu zuba jari domin tattauna manufar sauye-sauyen tattalin arzikin Najeriya da damar zuba jari a ƙasar, da kuma rawar da Afirka za ta taka wajen gina makomar tattalin arzikin duniya mai ɗorewa da haɗin kai.

    Ana sa ran Shettima zai koma Najeriya bayan kammala dukkan ayyukansa a taron na Davos.

  12. Majalisar Rivers ta buƙaci kotu ta binciki tsige Fubara

    ...

    Asalin hoton, Rivers State Assembly

    Majalisar dokokin jihar Rivers ta buƙaci babban alƙalin jihar ya kafa kwamitin bincike kan zargin aikata manyan laifuffuka da ake yi wa gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakiyarsa, Ngozi Odu.

    ‘Yan majalisar sun ɗauki matakin ne a ranar Juma’a bayan zaman da suka yi a Fatakwal, babban birnin jihar, tare jaddada aniyarsu ta ci gaba da shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa daga muƙamansu.

    Da yake jawabi a zaman, Shugaban masu rinjaye na majalisar kuma wakilin mazaɓar Akuku-Toru ta daya, Major Jack, ya ce dalilin ci gaba da shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa shi ne yadda suka ci gaba da saɓa wa ƙundin tsarin mulki tare da nuna rashin girmamawa ga majalisar dokoki.

    Ya ce duk da shiga tsakani da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, gwamnan da mataimakiyarsa ba su mayar da martani kan sanarwar tsigesu da za a yi da aka miƙa musu ba, kuma ba su ɗauki wani mataki ba domin kare kansu daga zarge-zargen da aka yi musu.

    Major Jack ya buƙaci kakakin Majalisar da ya ba da damar ci gaba da shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa wanda ya saka majalisar ta yanke shawarar kiran ɓabban alƙalin jihar da ya kafa kwamitin bincike domin yin bincike a kansu da zargin da ake musu.

    A halin da ake ciki kuma, ‘yan majalisa hudu da a baya suke neman a dakatar da shirin tsige gwamnan, sun janye kiran nasu tare da bayyana cikakken goyon bayansu ga ci gaba da shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa.

  13. ECOWAS ta naɗa sabon kwamandan sojoji a Gambia

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika wato ECOWAS ta naɗa sabon kwamandan sojoji a Gambia, Kanal Aliou Tine, wanda ya maye gurbin Kanal Ndiagne Diouf.

    Kanal Tine ya yi alƙawarin inganta tsaro a yankin da kuma tallafawa hukumomin gida don tabbatar da zaman lafiya a zaɓen watan Disamba na wannan shekarar.

    Bikin mika ragamar shugabanci, wanda ya haɗa da musayar tutocin umarni ya gudana ne a hedkwatar sojojin ECOWAS a Bakau.

    A cewar sanarwar ECOWAS ranar Alhamis, “An tabbatar wa Kanal Tine da cikakken goyon baya daga hedkwata da sauran kwamandojin runduna domin tabbatar da nasarar a ayyukan tsoma bakin soja na ECOWAS a Gambia da ake kira da ECOMIG.

    Kanal Diouf, wanda ya sauka daga muƙamin, ya ce a lokacinsa, an bayar da taimakon kiwon lafiya ga sama da mutum 8,000 da gudanar da fiye da ayyukan tsaro 100, da kuma dakarun sintiri fiye da 40 tare da jami’an tsaron Gambia.

    Duk da haka, kasancewar rundunar a ƙasar har yanzu na haifar da muhawara inda wasu ke ganin aikin su ya kammala kuma ya kamata su ja da baya, yayin da gwamnati da wasu ke jayayya cewa tsohon shugaban ƙasar Yahya Jammeh, wanda yanzu yake gudun hijira a Equatorial Guinea ya nuna anniyarsa ta komawa ƙasar .

  14. Wane ne Abba Atiku, ɗan jagoran adawar Najeriya da ya koma APC?

    ...

    Asalin hoton, Atiku Abubakar/X

    A ranar Alhamis ne Abubakar Atiku Abubakar (Abba) ya sanar da matakinsa na komawa jam'iyyar APC da kuma shan alƙawarin goyon bayan Bola Tinubu a zaɓen 2027, bayan ficewa daga jam'iyyar PDP, wadda a ƙarƙashinta ne mahaifinsa Atiku Aubakar ya tsaya takarar shugaban ƙasa.

    Hakan ya zo wa al'umma da dama da mamaki ganin adawar da ke tsakanin mahaifin Abba, wato Atiku Abubakar da shugaban ƙasa mai ci Bola Tinubu.

    Abba Atiku ya sanar da matakin nasa ne a wata ziyara da ya kai ofishin mataimakin shugaban majalisar dattawan ƙasar, Sanata Barau Jibril.

    A lokacin jawabin nasa, Abba Atiku ya ce ya koma APC ne saboda salon shugabanci da jajircewa na mataimakin shugaban majalisar dattawan.

  15. Limamin da ya tseratar da Kristoci a Plateau ya rasu

    ...

    Asalin hoton, US Embassy Nigeria

    Alhaji Abubakar Abdullahi, limamin Yelwa, Gindin Akwati a Barikin Ladi, Plateau, wanda ya yi fice a shekarun baya wajen kare mabiya Kirista daga kisa a rikicin Jos, ya rasu a daren Alhamis bayan fama da rashin lafiya.

    Ɗan autan marigayin, Saleh Abdullahi Abubakar, ya tabbatar wa da BBC cewa malamin ya rasu ne da misalin ƙarfe 9 na dare yana da kimanin shekara 90 a duniya.

    Saleh ya ce mahaifinsa ya yi fama da rashin lafiya ta ciwon zuciya inda aka kwantar da shi a asibiti a Filato.

    "Har an sallame shi bayan jinya a asibiti saboda ya koma gida, sai bayan wajen wata uku zuwa huɗu ne ciwon ya tashi, sai muka mayar da shi asibiti a duba shi a makon da ya gabata, daga nan ne suka sake kwantar da shi wanda daga bisani ya rasu jiya da dare."

    Ɗan ya ce an riga an mayar da gawar shi gida a Yelwa, Gindin Akwati da ke Barikin Ladi domin yi masa jana'iza da ƙarfe biyu bayan sallar Juma'a.

    Gwamnan Jihar Plateau, Barr. Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana jimami kan rasuwar limamin, inda ya bayyana rashin a matsayin babban rashi ga jihar baki ɗaya.

    A cikin sakon ta’aziyyarsa, Gwamna Mutfwang ya bayyana marigayin a matsayin jajirtacce wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai, da kare mutane musamman mata da yara.

    Gwamna Mutfwang ya ce rasuwar limamin rashi ne babba ga iyalinsa da al’ummarsa, da kuma jihar Plateau gaba ɗaya.

    Ɗan marigayin ya ce mahaifinsa ya samu karramawa daban-daban bayan tseratar da Kiristoci da ya yi a wani rikicin Jos, ciki har da zuwa hajji sau biyu da kuma lambobin karrama daga gwamnatin Buhari.

    Marigayin ya rasu yana da ‘ya’ya 19 da suke raye, ciki har da maza 12 da mata 7, sannan ya auri mata uku inda biyu daga cikinsu sun rasu.

  16. Jam'iyyar Issa Tchiroma za ta ƙaurace wa zaɓen ƴan majalisa a Kamaru

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jagoran adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya ce jam’iyarsa za ta ƙaurace wa zaɓen ƴan majalisa da na gundumomi na wannan shekarar, bayan da ya zargi gwamnatin ƙasar da ƙoƙarin “ƙwace ikon majalisa.”

    A cikin wata sanarwa da kakakinsa ya fitar, Tchiroma Bakary - wanda ke zaman gudun hijira a Gambia - ya ce mambobin jam’iyyarsa ta CNSF ko kowace jam’iyya ta siyasa da ke shirin shiga zaɓen za su zama masu goyon baya ga rashin gaskiya kuma suna da hannu a ciki.

    Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da wasu rahotonni ke cewa Bakary na duba yiwuwar komawarsa Kamaru, bayan ya tsere zuwa Gambiya bayan yayi iƙirarin lashe zaɓen shugaban ƙasar da ya gabata.

    Tchiroma wanda ke kiran kansa da "shugaban Kamaru na gaskiya" ya jaddada cewa ba shi da niyyar sarayar da nasarar da ya samu a zaɓen da ya gabata

    Duk da zarge-zargen maguɗi da rashin gaskiya a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a shekarar da ya gabata, kotun tsarin mulki ta Kamaru ta bayyana Paul Biya, a matsayin wanda ya ci zaɓen shugaban ƙasa na 12 ga Oktoba.

  17. An gano makeken kabarin ƴan ci-rani a Libya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a gabashin Libya sun gano gano wani makeken kabarin da aka binne ƴan ci-rani 21.

    Wannan lamari ya biyo bayan wani farmaki da aka kai a wani gidan gona kusa da garin Ajdabiya inda aka ceto wasu mutane masu rai waɗanda ke nuna alamun an azabtar da su.

    Rahotannin kamfanin dillancin labarai na Reuters sun nuna cewa jami’an tsaro sun ce an gano wannan makeken kabarin ne kimanin kilomita 10 daga kudu maso gabashin garin, bayan samun bayanan sirri cewa wasu ƴan ci-rani daga yankin Sub-Saharan Afirka suna tsare a gidan.

    Wani jami’i ya bayyana cewa an ceto waɗanda suka tsira da suka haɗa da maza da mata da yara daga gidan.

    Wasu daga cikinsu na ɗauke da tabon azabtarwa a jikin su inda aka kai su asibiti kuma suka bayar da rahoton cewa wasu daga cikinsu sun ɓace.

    An kama mai gidan, wanda ya amsa cewa akwai makeken kabarin ɗauke da gawarwaki a gonarsa.

    Masu bincike na ci gaba da tantance yadda waɗannan mutane suka mutu.

    Libya ta daɗe tana zama muhimmin wuri ga ƴan ci-rani da ke ƙoƙarin tsallaka wa zuwa Turai, musamman tun bayan rushewar gwamnatin Muammar Gaddafi a 2011 da ya jefa ƙasar cikin rashin tabbas.

  18. Kotu za ta yanke hukunci kan tsohon shugaban ƙasar Koriya ta Kudu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    A yau ne wata kotu a Koriya ta Kudu zata yanke hukunci kan shari’ar da ake yi wa tsohon shugaban kasa, Yoon Suk Yeol, kan dokar sojin da ya sanya wadda ba ta yi tasiri ba.

    Idan aka same shi da laifin wasa da mulki, zai iya fuskantar hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 10.

    Haka zalika, tsohon shugaban zai fuskanci shari’o’i da dama, ciki har da tuhume-tuhume kan tarihi da ayyukan da ya yi yayin mulkinsa, wanda ya sa masu shigar da ƙara suka nemi a yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

    Kotun za ta tantance hujjojin da aka gabatar da kuma yadda dokokin kasa da kasa ke kallon irin wannan laifi, kafin ta yanke hukunci.

  19. Ba mu kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi ba - Hukumar harajin Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar Haraji ta Najeriya NRS ta bayyana cewa rahotanni da ke yawo a wasu sassa na kafofin yaɗa labarai game da cewa an kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi wato VAT ba gaskiya bane.

    Hukumar ta ce wannan bayani na yaudara ne kuma babu sabuwar haraji i da aka kafa a kan kwastomomi aka ce wajibi ne sai sun biya.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X.

    NRS ta bayyana cewa tun farko dama wannan haraji na aiki a ƙarkashin dokar haraji na Najeriya da aka kafa tun shekaru da dama inda bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi ke cire kuɗin gudanarwa, da na hidima da suka yi da sauran kuɗaden da suke cirewa, ba sabon haraji bane.

    Ta bayyana cewa duk wani bayanin da ke cewa gwamnati ta umarci bankuna da su fara cire harajin kashi 7.5 a kan kudin da aka cire ko aka tura da suka kai naira 100,000 ba dai dai bane.

    Saboda haka ne hukumar ta buƙaci jama’a da masu ruwa da tsaki da su daina yarda da labaran da ba su da tushe, su kuma dogara ga sanarwar hukumar kai tsaye don samun sahihin bayani.

  20. Martanin Atiku kan komawar ɗansa APC

    ...

    Asalin hoton, Atiku Abubakar/X

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ce shawarar da ɗansa Abba Atiku Abubakar ya yanke na barin jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki mataki ne na ƙashin kansa.

    A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Atiku ya ce a tsarin dimokuraɗiyya irin waɗannan lamuran ba sabon abu ba ne, ko da kuwa siyasa ta haɗu da alaƙar iyali.

    Atiku ya ƙara da cewa "A matsayi na na ɗan dimokiraɗiyya, ba na tilasta wa ’ya’yan na ra’ayi a kan abubuwa da suka shafi irin wannan lamarin haka kuma bazan tilasta wa ’yan Najeriya ba."

    Atiku ya jaddada cewa ra’ayin ɗansa ba zai sa shi canza manufarsa wajen aiki domin kawo ingantacciyar shugabanci ba.

    Abba Atiku dai ya sanar da barinsa PDP zuwa APC a ranar Alhamis, yayin wata ziyara da ya kai ofishin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan ƙasa, Sanata Barau Jibril.

    A jawabin nasa, Abba ya bayyana cewa dalilin sauya sheƙarsa shi ne sha’awarsa ga salon shugabanci da jajircewar Sanata Barau.

    Abba Atiku ya ce zai yi aiki tare da Sanata Barau domin ganin an sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027.

    “Don haka zan yi aiki da Sanata Barau domin tabbatar da nasarar sake zaɓen Shugaba Tinubu a karo na biyu,” in ji shi, kamar yadda Sanata Barau ya wallafa a shafinsa na X.

    Atiku ya kuma ce abin da ya fi damunsa shi ne rashin kyakkyawan shugabanci na APC da kuma matsin tattalin arziki da zamantakewa da jam’iyyar ta jefa ’yan Najeriya a ciki inda ya ce zai ci gaba da aiki tare da masu kishin ƙasa domin samar da ingantacciyar shugabanci ga al’umma.