An mayar da gawar tsohon shugaban Zambia Edgar Lungu ƙasarsa
Gwamnatin Zambia ta ce an dawo mata da gawar tsohon shugaban ƙasar Edgar Lungu, bayan watanni goma ana taƙaddama kan dawo da gawar daga Afirka ta Kudu.
Gwamnatin Zambia na so a gudanar da janaizar girmamawa ga Mista Lungu a babban birnin ƙasar Lusaka, wani abu da iyalan sa suka nuna ƙin amincewa.
Rahotanni sun bayyana cewa an ɗauki gawarsa ne daga wani wurin ajiyar gawa a daren Laraba ba tare da sanin iyalansa ba.
Babban lauyan gwamnati na Zambia ya ce babbar Kotun Pretoria ce ta miƙa gawar mista Lungu ga gwamnati, bayan da iyalan sa suka yi watsi da batun ɗaukaka ƙarar da suka shigar na buƙatar a soke hukuncin cewa a binne tsohon shugaban ƙasar a Lusaka.