Harin Isra'ila "da gan gan" a kudancin Lebanon ya hallaka wata ƴar jaridar ƙasar

Asalin hoton, AP
Firaministan Lebanon, Nawaf Salam, ya zargi Isra'ila da aikata laifukan yaƙi bayan an sake kashe wata 'yar jarida 'yar Lebanon a kudancin kasar.
Wani harin Isra'ila ta sama ne ya samu Amal Khalil a lokacin da ake cewa tana kokarin tsira a wani gida.
Jami'an Lebanon sun ce, da niyya Isra'ila ta kai harin kan 'yar jaridar.
Firaministan ya ce sojin Isra'ila sun hana ma'aikatan agaji kaiwa ga wajen da suka kai harin.
Ya ce kasarsa za ta kai batun gaban taruka na duniya.
Sojin Isra'ila sun musunta kai hari kan 'yan jarida ko hana ma'aikatan agaji kai dauki wajen, kuma sun ce suna gudanar da bincike.


