Tarko INEC ke son naɗa mana kuma ba za mu kamu ba - ADC

Asalin hoton, ADC
Jama'iyyar adawa ta ADC ta haɗakar ƴan adawar Najeriya ta zargi hukumar zaɓen ƙasae INEC ta naɗa mata tarko ta hanyar hanyar yunƙurin dakatar da ita daga gudanar tarukanta domin zaɓen shugabanninta.
ADC - tsagin David Mark - ta jaddada aniyar ci gaba da tsare-tsarenta na gudanar da zaɓukan shugabanninta na jihohi da babban taron jam'iyyar na ƙasa, saɓanin gargaɗiin da hukumar zaɓen ƙasar ta yi, yayin da batun rikicin shugabanci ke ci gaba da munana a jam'iyyar
A baya-bayan nan ne dai INEC ta gargaɗi jam'iyyar da kada ta gudanar da tarukan jam'iyyar da za su zaɓi shugabanninta don gudan Matsala.
Cikin wata hira da gidan talbijin na Arise a ranar Juma'a shugaban hukumar Farfesa Joash Amupitan ya ce kotu ta riga ta dakatar da jam'iyyar daga gudanar da komai har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan rikicin shugabancin jam'iyyar.
Sai dai Kakakin jam'iyyar, Faisal Kabir ya shaida wa BBC cewa, mataki wata ƙualliya ce domin kafa wa jam'iyyar tarko a hana ta yin tarukan ta yadda daga baya za a ce ba ta da shugabanci, don haka ba za ta shiga zaɓen 2027 ba.
''Tarko aka kafa mana da wannan, ai su manyan tarukan jam'iyyu, wajibi ne a doka, kuma suna da lokacin yinsu, idan wannan lokacin ya ƙure shikenan'', in ji shi.
Ya ƙara da cewa abin da dokokin Najeriya suka ce shi ne ka sanar da INEC taron jam'iyyarka kwana 21 kafin ranar taron, mu kuma mun sanar da ita.




