KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman bayanai dangane da yaƙin Iran da ma sauran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na 22/04/2026

Rahoto kai-tsaye

Aisha Aliyu Jaafar

  1. Ma'aikatar lafiya ta Cross River ta tabbatar da samun wani ɗan China mai ɗauke da cutar Corona

    ma'aikaciyar lafiya rike da allura

    Asalin hoton, Reuters

    Ma'aikatar lafiya ta jihar Cross River da ke kudu maso kudancin Najeriya ta tabbatar da samun mai ɗauke da cutar Corona a jihar.

    Kwamishinan lafiya na jihar Dakta Henry Ayuk, wanda ya tabbatar da hakan ga manema labarai, ya ce an tabbatar da hakan ne a ranar 17 ga watan Afrilun 2026, kuma wani ɗan China da ya shigo ƙasar ranar 17 ga watan Maris ne ke ɗauke da cutar.

    Ya ce jikin mara lafiyan ya yi tsanani ne a lokacin da ya ke wani asibiti da ke karkashin ofishin da ya ke aiki, kafin daga bisani aka garzaya da shi asibitin koyarwa na jami'ar Calabar.

    A cewarsa bayan yi masa gwaje gwaje a asibitin ne aka tabbatar da cewa yana ɗauke da cutar, kuma a yanzu haka an killace shi.

    Ya kuma buƙaci yan jihar da kar su tayar da hankalinsu, a cewarsa suna duk mai yiwuwa na hana cutar yaɗuwa, da ma duk wata cuta a jihar.

    Hukumar hana yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC ta tabbatar da lamarin, kuma ta ce tana aiki da gwamnatin jihar domin shawo kan lamarin.

  2. Iran ta kai hari kan wasu jiragen ruwa a Mashigar Hormuz

    jiragen ruwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun Iran sun kai hari kan wani jirgin dakon kaya mallakin Girka a Mashigar Hormuz.

    Bisa bayanan da BBC ta gani, an gano cewa jirgin Epaminondas ne.

    Tun da farko an bayyana wa matuƙin jirgin cewa yana da izinin wucewa.

    Amma daga bisani wani jirgin ruwa yaƙin dakarun juyin juya halin Iran ya buɗe masa wuta.

    A gefe guda kuma wata hukumar kula da sufurin jiragen ruwa na Birtaniya (UKMTO) ta ruwaito cewa an buɗe wuta kan jirgin na biyu a mashigar.

    Jirgin dakon kayan na ƙoƙarin barin yankin ne a lokacin da aka kai masa hari, a yanzu kuma ana tsare da shi kan ruwan.

    Rahotanni sun ce jami'an jirgin na cikin ƙoshin lafiya.

  3. Sojojin hayan Colombia masu samun goyon bayan Haɗaddiyar daular Larabawa na taimaka wa RSF - Rahoto

    Wani sabon rahoto ya nuna cewa sojojin haya na Colombia da ke samun goyon bayan Haɗaddiyar daular Larabawa sun taimaka wa dakarun kungiyar RSF ta Sudan sake kama birnin el-Fasher na Sudan a shekarar da ta wuce.

    Babban mai binciken ya ce wannan ne bincike na farko da ya tabbatar da cewa Hadaddiyar daular Larabawa tana da alaka da kungiyar ta RSF, ba tare da wata tantama ba.

    Wakiliyar BBC ta ce kungiyar ta ce bayanan sun nuna alaka na daban-daban da Hadaddiyar Daular Larabawar.

    Kungiyar da ta yi binciken - Critical Insights Group, ta ce Hadaddiyar daular Larabawa da sojojin na Colombia na da alhakin laifukan azabtarwa da dakarun RSF suka yi a lokacin sake kwace birnin, wanda yana daya daga cikin mummunar ta'asa da aka yi a yaƙin basasar na Sudan.

    Har kullum dai Hadaddiyar daular na musanta taimaka wa RSF.

  4. Gwamnan Kano ya zaɓi Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakinsa

    Sule Garo

    Asalin hoton, Murtala Sule Garo/ FACEBOOK

    Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya aika sunan Murtala Sule Garo domin neman amincewa da shi a matsayin sabon mataimakinsa.

    A cikin wata sanarwa da babban jami'in yaɗa labarai na gwamnan Mustapha Muhammad ya fitar, ya ce bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki, Gwamnan ya buƙaci majalisar dokokin jihar ta amince da naɗin Garo.

    Sanarwar ta kuma ce Gwamnan ya gabatar da sunansa ne a ƙoƙarin gwamnatin na karfafar aikin gwamnatin da kuma inganta gudanar da ayyuka a jihar ta Kano.

    Wannan na zuwa ne bayan da tsohon mataimakin gwamnan Kwamared Abdulsalam Gwarzo ya yi murabus a baya bayan nan.

    Ana ganin Gwarzo ya ajiye aikin ne bayan ƙin amincewa ya bi gwamnan jihar zuwa jamiyyar APC bayan ficewa daga NNPP duk da shan matsi.

  5. MDD ta yi maraba da tsawaita dakatar da buɗe wuta a Iran da Amurka ta yi

    Antonio Guterress

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Majalisar Dinkin Duniya ya yi maraba da sanarwar da Shugaba Trump ya yi ta tsawaita dakatar da buɗe wuta da Iran har sai an kammala tattaunawa.

    Mai magana da yawun Antonio Guterres, ya bayyana hakan a matsayin mataki mai alfanu, da zai bayar da damar samun maslahar diflomasiyya.

    A wani saƙo da ya sanya a shafinsa na sada zumunta Trump ya yi gargadin cewa, Amurka za ta ci gaba da toshe tashoshin jiragen ruwa na Iran, har sai Iran ɗin ta gabatar da abin da ya kira matsayi na bai ɗaya a kan tattaunawar.

    Wakiliyar BBC ta ce duk tsawon lokacin wannan rikici Trump na amfani da shafin sada zumunta da sanarwa a talabijin ya yi gargadi ga Iran.

    Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif wanda ke shiryawa da karɓar baƙucin tattaunawar ya ce yana fatan ɓangarorin biyu za su ci gaba da mutunta dakatar da buɗe wutar.

  6. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barka da safiyar yau Laraba.

    Yau ma kamar kullum mun dawo muku da shafin namu na kai tsaye inda muke kawo muku muhimman labarai dangane da al'amuran yau da kullum, musamman kan yakin Iran da Amurka da kuma kan Najeriya.

    Da fatan za ku ci gaba da kasancewa da shafin da ma sauran shafukan sada zumunta na BBC Hausa kamar Facebook, Instagram, X, da kuma YouTube.