Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sauran sassan duniya, Lahadi 5/4/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sauran sassan duniya, Lahadi 5/4/2026

Taƙaitattu

  • Amurka ta ceto matuƙin jirginta da ya ɓace a Iran
  • Ƙasashen da al'umma suka fi farin ciki a duniya cikin shekara 2026
  • Iran ta yi watsi da wa'adin kwana biyu da Trump ya sanya mata
  • Hare-haren Isra'ila sun kashe mutum biyar a Iran
  • Za mu yi taronmu na ADC ko da INEC ko babu - Atiku
  • Iran na ci gaba da zafafa hare-hare a faɗin yankin Gulf
  • Sojojin Isra'ila sun ce sun kai harin bama-bamai kan cibiyoyin Hezbollah a Beirut

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Bidiyon wasu jiragen yaƙin Amurka da aka lalata a Iran

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun wallafa wasu hotuna da bidiyo na tarkacen wasu jiragen da aka lalata a lokacin aikin neman matuƙin jirgin yaƙin Amurka na F-15 a Iran.

    A cewar kafofin yaɗa labaran Amurka, a lokacin aikin ceton wasu jiragen jigilar mayaƙa biyu da ya kamata ya ɗauki kwamandoji da matuƙin jirgin zuwa wuri mai aminci sun fuskanci matsala.

    Jaridar New Yorks Times ta ce kan haka ne ''sojojin Amurka suka lalata jiragen biyu domin kada su faɗa hannun dakarun Iran.''

    To amma a cewar sansanin sojin sama na Khatam Al-Anbia na Iran ya ce dakarun ƙasar sun ''harbi jiragen maƙiya a kudancin Isfahan, ciki har da masu saukar ungulu biyu samfurin Black Hawk da kuma jirgin jigilar dakaru na C-130.

  2. Matuƙin jirgin da muka ceto ya ji 'munanan raunuka' - Trump

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya wallafa wasu bayanai a shafinsa na sada zumunta game da aikin ceto ɗaya matuƙin jirgin yaƙin ƙasar da Iran ta harba.

    Mista Trump ya ce "mun samu nasarar kuɓutar da mutumin, wanda ya samu munanan raunuka, amma kuma ya nuna jarumta, mun same shi a atsakiyar tsaunukan Iran. Su ma sojojin Iran masu yawan gaske na cikin nemansa domin kama shi, kuma saura ƙiris burinsu ya cika''.

    Soja ne mai muƙamin Kalan da Trump ya bayyana da ''wanda ake matuƙar martabawa''.

    "Neman jami'in, aiki ne ne mai cike da fargaba saboda hatsarinsa ga 'mutumin da kuma akayan aiki'.

    Mun yi aikin neman ne bayan nasarar gano jami'in farko wanda shi ne aihinin matuƙin jirgin, bayan kwashe sa'o'i bakwai.

    "Abin burgewa kowa ya nuna jarumta da ƙwarewa, zan gabatar da taron manema labarai tare da sojoji a ofishina ranar Litinin'', in ji shugaban na Amurka.

  3. Jami'an tsaro sun ƙaddamar da farautar mutanen da aka sace a Zamfara

    Hadin gwiwar jami'an tsaron Najeriya sun ƙaddamar da farautar wasu mutane da ƴanbindiga suka sace a garin Kurfa da ke yankin ƙaramar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.

    A ranar Juma'a ne ɗan majalisar wakilai na tarayya da ke wakiltar yankin ya shaida wa BBC cewa wasu mahara sun shigar garin Kurfa tare da sace fiye da mutum 150.

    Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, DSP Yazid Abubakar ya ce maharan sun je ƙauyen ne a kan babura inda suka riƙa harbin kan mai tsautsayi, lamarin da ya haifar da firgici tsakanin al'ummar garin.

    Sanarwa ta ce haɗin gwiwar jami'an tsaro da suka haɗa da ƴansanda da sojoji da sauran jami'an tsaro na ci gaba da farautar maharan.

    Kakakin ƴansandan ya ci gaba da cewa tawagar jami'an tsaron ta gano wasu mutanen da suka samu kuɓuta daga maharan, waɗanda yanzu haka ke karɓar magani asibiti.

    DSP Yazid ya ce kawo yanzu ba su san haƙiƙanin adadin mutane da ƴanbindigar suka sace ba, yayin da suke ƙoƙarin maido da zaman lafiya a yankin.

  4. Sojojin Isra'ila sun ce sun kai harin bama-bamai kan cibiyoyin Hezbollah a Beirut

    Sojojin isra'ila sun ce sun ƙaddamar da sabbin hare-hare kan cibiyoyin Hezbollah a birnin Beirut bayan gargaɗin da suka yi wa mazauna kudancin babban birnin Lebanon ɗin cewa su tashi cikin gaggawa da safiyar nan.

    A nata ɓangare Hezbolla, wadda ke samun goyon bayan Iran ta ce ta kai hare-haren makamai masu linzami zuwa kudancin Isra'ila, kodayake IDf ta ce ta kakkaɓo su, a cewar kafofin sda zumuntar Isra'ila.

    Musayar wutar na zuwa ne sa'o'i bayan Hezbollah ta ce ta kai harin makamai mai linzami kan jirgin ruwan yaƙin Isra'ila a gaɓar tekun Lebanon cikin dare ta hanyar m

    A cewar kafofin yaɗa labaran Isral'ila, rundunar IDF ta ce ba ta san da labarin harin ba.

  5. Iran ta ce ta kakkaɓo jirgin Amurka maras matuƙi lokacin neman sojin ƙasar

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayar da rahoton cewa dakarun juyin juya halin ƙasar sun kakkaɓo wani jirgin Amurka maras matuƙi a lokacin da yake aikin neman sojan saman Amurkan nan da Iran ta harbo jirgin da yake ciki.

    Jirgin marar matuƙi ya faɗo ne a lardin Isfahan da ke kudancin ƙasar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Fars ya ambato ofishin yaɗa labaran rundunar ta IRGC na cewa.

    Kawo yanzu Amurka ba ta tabbatar da rahotonnin ba.

  6. Iran na ci gaba da zafafa hare-hare a faɗin yankin Gulf

    Iran ta ci gaba da ƙaddamar da hare-hare kan muhimmancin abubuwan more rayuwa a faɗin yankin Gulf a matsayin martani kan abin da ta kira hare-haren Amurka da Isra'ila kan wata cibiyar masana'antun ƙasa.

    A birnin Abu Dhabi na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, jami'ai sun ce ƙoƙarin kashe gobarar da ta tashi a manyan kamfanonin man fetur, wadda ta tashi sakamakon ɓaraguzan makaman linzami da ƙasar ta kakkaɓo.

    A Kuwait ma jirage marasa matuƙa na Iran sun kai hari tare da lalata cibiyoyin samar da lantarkin ƙasar biyu da cibiyar tace ruwa, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin duhu.

    Haka a Bahrain, kamfanin samar da makamashin ƙasar ya ce harin Iran ya haifar da tashin gobara a ɗaya daga cikin rumbunan ajiyar mai, kodayake daga baya an kashe ta.

    Ko a ranar Asabar ma, wani hari kan cibiyar makamashin man fetur a kudu maso yammacin Iran ya kashe mutum biyar.

  7. Za mu yi taronmu na ADC ko da INEC ko babu - Atiku

    Jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar ya ce sabuwar haɗakarsu ta ADC za ta yi tarukanta ko da sahalewar INEC ko babu.

    Cikin hirarsa da BBC, Atiku ya ce abin da doka ta ce shi en su shaida wa INEC aniyarsu ta yi taro.

  8. Fafaroma Leo na bikin Easter karon farko a matsayin jagoran Katolika

    Fafroma Leo na bikin ranar Easter ta farko a matsayinsa na jagoran Cocin Katolika a dandalin St Peters

    Dubban masu ibada ne suka taru a dandalin - wanda aka ƙawata da fulawoyin da aka ƙiyasta za su kai 65,000.

    Bayan taron ibadar, fafaroman zai gabatar da addu'o'i na musamman da ake yi wa laƙabi da ''Urbi et Orbi'' ga birnin Roma da ma duniya baki ɗaya.

    A baya-bayan nan Fafaroma Leo ya yi magana game da fatansa na Shugaba Trump ya duba yiwuwar kawo ƙarshen yaƙin Iran.

  9. Hare-haren Isra'ila sun kashe mutum biyar a Iran

    Rahotanni daga Iran na cewa hare-haren sama da Israel ta kai kan wata babbar cibiyar sarrafa sinadarai sun kashe aƙalla mutum biyar.

    Sojojin Isra’ila sun ce sun kai harin ne kan cibiyar Mahshahr saboda ana amfani da ita wajen ƙera muhimman sassan makamai masu linzami.

    Tun da farko a jiya Asabar, an kashe wani jami’in tsaro a wani harin na daban da aka kai kusa da tashar nukiliya ta Bushehr.

    Kamfanin Rosatom na Rasha da ke kula da wurin ya ce ya kwashe kusan ma’aikata 200 daga yankin.

  10. Iran ta yi watsi da wa'adin kwana biyu da Trump ya sanya mata

    Iran ta yi watsi da wa’adin da Shugaban Amurka Donald Trump ya gindaya mata, na cimma yarjejeniya ko kuma buɗe mashigin Hormuz ba tare da ɓata wani lokaci ba.

    Tun da fari, Mista Trump ɗin ya yi barazanar saukar wa ƙasar abin da ya kira “ruwan wuta'' idan har ba ta amince da yarjejeniya cikin kwanaki biyu ba.

    A wata sanarwa, shugaban rundunar ƙoli ta sojin Iran, Janar Ali Abdollahi, ya bayyana Trump ɗin a matsayin “firgici da wauta''.

    Ya kuma gargaɗin cewa abun da Trump ɗin ke fatan saukar wa Iran a ƙarshe zai ƙare ne a kan Amurka''

    Ya ƙara da cewa idan Amurka ta kai hari kan muhimman kayayyakin more rayuwa na Iran, to Tehran za ta kai hari kan wuraren da sojojin Amurka da Isra’ila ke amfani da su “ba tare da wani shamaki ba''

  11. Amurka ta ceto matuƙin jirginta da ya ɓace a Iran

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce sojojin ƙasar sun ceto matuƙin jirgin yaƙin nan na ƙasar da ya ɓace a kudancin Iran, bayan an harbo jirginsa ƙirar F-15 a ranar Juma’a.

    A wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Mista Trump ya ce sojojin sun gudanar da ɗaya daga cikin ayyukan ceto mafi jarumta a tarihin Amurka.

    BBC ta fahimci cewa an yi ƙazamin artabu tsakanin sojojin Amurka da na Iran yayin wannan aiki.

    Wasu hotunan bidiyo a shafukan sada zumunta sun nuna yadda ɗaruruwan mutane ke ta tuɗaɗa zuwa yankin mai yawan tsaunuka a kudu masu yammacin Iran don taimakawa wajen gano inda sojan yake.

  12. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku domin kawo muku sabbin labarai.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.