Jagororin masu boren farashin man fetur 100' sun shiga hannu a Iran
Asalin hoton, Reuters
Hukumomin shari'a a Iran sun ce sun kama jagororin masu bore kan hauhawar farashin man fetur su kimanin 100 a kasar.
Wata sanarwa da ma'aikatar shari'a ta fitar ta ce rundunar sojojin kasar mai karfin iko ta Revolutionary Guards ce ta zakulo su "a sassan kasar daban-daban"
Matakin ya biyo bayan saka takunkumi da Amurka ta yi wa ministan sadarwa na kasar saboda dode hanyoyin sadarwa na intanet a yayin da ake boren.
Amnesty International ta ce an kashe fiye da mutum 100 a lokacin gumurzun da ya faru a biranen kasar masu yawa.
Amma hukumomin Iran sun ce mutum 12 ne suka rasa rayukansu.
Shugaba kasar ya yi wani jawabi ranar Laraba, wanda a ciki yake cewa kasar ta "sami nasara kan wani shirin da makiya suka kitsa", kuma ya ce Amurka, da Isra'ila da Saudiyya ne suka shirya tashin hankalin.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai