Masu zanga-zanga a Sudan sun bijire wa dokar hana fita
Asalin hoton, AFP
Dubban masu zanga-zanga a Sudan sun bijirewa dokar hana fita da sojojin kasar suka saka inda suka kwana kan tituna.
A ranar Alhamis ne sojojin suka hambarar da gwamnatin Omar al-Bashir wanda ya shafe kusan shekaru 30 kan karagar mulki.
Amma masu zanga-zangar sun bayyana cewa sojojin da suka yi juyin mulki da su aka dama a gwamantin al-Bashir.
Wannan sabuwar kurar da ta ta so a Sudan na sa jama'a na fargabar yiwuwar fito na fito tsakanin masu zanga-zangar da kuma jami'an tsaro a kasar.
Akwai kuma babbar barazanar da ake ganin cewa jami'an tsaro tsakaninsu na iya juya wa kawunansu baya su yaki juna kamar yadda Editan BBC na Afirka Will Ross ya bayyana.
A yanzu haka dai Majalisar Dinkin Duniya da kuma Kungiyar Tarayyar Afrika sun yi kira da a zauna lafiya.
Me masu zanga-zangar ke cewa?
Har zuwa yanzu, akwai dubban masu zanga-zangar da suka yi zaman dirshen a gaban shelkwatar rundunar sojojin kasar inda suke gudanar da zanga-zangar.
Murnar da aka yi a ranar Alhamis bayan sanarwar da aka yi ta juyin mulki a Sudan ta bar baya da kura sakamakon kiraye-kirayen da manyan kungiyoyi masu gudanar da zanga-zanga a kasar suke yi na a ci gaba da zaman dirshen a gaban shelkwatar sojojin kasar.
Sara Abdeljalil, daya daga cikin 'yan kungiyar da ke jagorantar zanga-zanga a kasar ta bayyana cewa ''wannan ci gaba da tsohon mulkin al-Bashir ne kawai, abinda yakamata mu yi shi ne mu ci gaba da gwagwarmaya.''
Tun a baya kungiyar mai jagorantar zanga-zangar ta bayyana cewa ba za su yadda wani daga cikin wadanda suka gudanar da mulkin kama karya ba ya jagoranci Sudan.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai