'Yan Israila na da 'yancin samun kasarsu - Yerima Salman
Asalin hoton, Getty Images
Yarima mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya amince cewa 'yan Israila na da 'yancin samun kasarsu.
A wani lamari da ya nuna sauyin matsayin Saudiyyar, Yerima Mohammed ya shaida wa mujallar Atlantic ta Amurka cewa 'yan Israila da Palasdinawa kowane na da 'yanci akan kasarsu.
A hukumance dai Saudiyya ba ta amince da kasar Israila ba, sai dai an dan samu kyautatuwar dangantaka ta bayan fage tsakanin kasashen biyu.
Kasashen biyu dai na kallon Iran a matsayin babbar barazana gare ta, baya ga mayakan kungiyoyi masu tada kayar baya.
A yanzu ana samun sauye-sauye a kasar Saudiya inda a baya kasar mai ra'ayin rikau ba ta cika tsoma baki ba cikin wasu harkokin yankin gabas ta tsakiya.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai
{{rankTranslation}}