Nigeria: An 'ceto jarirai sama da 200 da aka zubar' a Lagos
Asalin hoton, Getty Images
Gwamnatin jihar Lagos a Najeriya ta ce ta yi nasarar ceto jarirai 237 da aka zubar a sassa daban-daban na jihar.
Jarirn 106 maza ne, yayin da 131 kuma suka kasance mata, kuma an jefar da su ne a bara.
Jaridar Punch da Guardian, sun rawaito cewa, kwamishinan matasan jihar, Uzamat Akinbile-Yussuf, yana ganin cewa an kara samun yawaitar adadin jariran da aka tsinta a watannin baya-bayan nan.
Yara na baya-bayan nan da aka tsunta su ne guda 53 da aka zubar a kusa da wata bola a jihar.
Wani wakilin BBC a Najeriya ya ce akan jefar da jarirai ne saboda iyayensu talakawa ne ko kuma an haife su ne ba ta hanyar aure ba.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai
{{rankTranslation}}