Saudiyya ta nada Mancini sabon kociyanta
Asalin hoton, BBC Sport
An nada Roberto Mancini a matsayin sabon kocin Saudiyya makonni biyu bayan ya yi murabus a matsayin kocin Italiya.
Mai shekaru 58 ya jagoranci Italiya ta samu nasara a gasar Euro 2020, inda ta doke Ingila a bugun fanariti a wasan karshe a Wembley.
A karkashin Mancini tawagar Italiya ta kafa tarihin buga wasa 37 ba tare da an doke ta ba a jere, amma ta kasa samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2022.
Ya rattaba hannu kan kwantiragi har zuwa 2027. Wasansa na farko da zai jagoranta zai zama ranar 8 ga Satumba da Costa Rica a filin wasan St James' Park da ke birnin Newcastle.
A gasar cin kofin duniya da aka yi a bara a karkashin tsohon kociyan tawagar Herve Renard, Saudi Arabiya ta gigita Argentina da ci 2-1 a Qatar amma ta kasa tsallake matakin rukunin farko a gasar.
Mancini ya jagoranci Manchester City ta lashe gasar Premier na farko a shekara ta 2012, sannan ya jagoranci Fiorentina da Lazio da Inter Milan da Galatasaray da Zenit St Petersburg.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai