Sojin Najeriya sun kaddamar da yaki da laifi a intanet
Asalin hoton, HQ Nigerian Army
Rundunar sojin Najeriya ta kaddamar da yaki da laifuka a intanet, domin magance yaduwar labaran bogi wanda zai iya kawo rudani a zukatan mutane.
Babban hafsan sojojin kasan Najeriya Janar Tukur Yusuf Buratai, ya sanar da hakan a wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook.
Janar Buratai ya ce sabon sashen zai taimaka wajen yaki da al'amuran da suka shafi ta'addanci a intanet.
Ya kuma ce sojojin za su kaddamar da wata manhajar waya don taimakawa mutane wajen kai karar sojoji masu cin zarafin mutane.
Mutane za su iya sanya bidiyo a kan manhajar wayar don kafa hujja game da korafe korafensu, wanda za su iya dorawa ba tare da an san ko waye ya dora ba.
Babban Labari
Labarai na musamman
Labaran da suka fi shahara
Babu karin bayanai
{{rankTranslation}}