Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 10/04/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da kuma muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar Juma'a 10 ga watan Afrilun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello, Haruna Kakangi, Usman Minjibir

  1. Isra'ila na ci gaba da kai hare-hare a cikin Lebanon

    Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare kan ƙungiyar Hezbollah a Lebanon duk da kiraye-kirayen ƙasashen duniya na a dakata.

    Isra'ila ta umarci al'ummar kudancin Lebanon da su gaggauta ficewa domin kauce wa hare-haren da take shirin kaiwa.

    Hezbollah ita ma ta ce ta harba rokoki zuwa cikin Isra’ila a daren jiya da kuma yau Juma’a.

    Sai dai ana ƙoƙarin ci gaba da tattaunawar sulhu tsakanin Isra’ila da gwamnatin Lebanon, duk da cewa Beirut ta sake tabbatar wa BBC cewa masu shiga tsakani daga Lebanon ba za su halarci tattaunawa kai tsaye da Isra’ila ba sai an tsagaita wuta.

    Shugaban Hezbollah, Na'im Qassem, ya buƙaci gwamnatin Lebanon da ta daina yin abin da ya kira ɗaga kafa ga Isra’ila.

  2. Ƙofar Amurka a buɗe take idan Iran ta zo tattaunawa da kyakkyawar manufa - Vance

    Mataimakin shugaban Amurka JD Vance wanda yanzu haka ke kan hanyarsa ta zuwa Pakistan domin tattaunawar sasanci da Iran ya ce "ƙofar Amurka a buɗe take" idan har Iran ta je da "kyakkyawar manufa".

    Amma ya ƙara da cewa idan "suka yi yunƙurin yaudarar mu" ba za mu ɗaga musu ƙafa ba.

    Ya bayyana cewa shugaban Amurka Donald Trump ya ba shi sharuɗɗan da za a yi amfani da su wajen tattaunawar.

    Za a fara tattaunawar ne a birnin Islamabad na ƙasar Pakistan a ranar Asabar, kamar yadda mai magana da fadar shugaban Amurka, Karoline Leavitt ta sanar tun farko.

    Tawagar Amurka a wurin tattaunawar za ta haɗa da jakadan shugaba Trump na musamman Steve Witkoff da kuma Jared Kushner, to amma har yanzu ana jiran isar tawagar Iran a birnin Islamabad.

  3. Mataimakin shugaban Amurka ya kama hanyar zuwa tattaunawar sasanci

    Mataimakin shugaban ƙasar Amurka J.D Vance yana kan hanyar zuwa Pakistan a shirye-shiryen tattaunawar sasanci da za a fara tsakanin ƙasarsa da Iran a gobe Asabar.

    Ya ce ya ƙagu a fara tattaunawar ta birnin Islamabad sannan yana fatan a samu fahimtar juna.

    Tun farko, Pakistan ta yi gargaɗin cewa buƙatun ƙasashen biyu game da yarjejeniyar sun yi hannun riga sosai.

    Dukkanin ɓangarorin biyu na zargin juna da karya sharuɗɗan tsagaita wuta da aka cimma a farkon wannan mako.

    Iran ta dage kai da fata cewa wajibi ne tsagaita wutar da aka cimma ta haɗa har da Lebanon, ita kuma Amurka ta zargi Iran da ƙin buɗe mashigar Hormuz ga jiragen dakon man fetur na duniya.

  4. Majalisar dokokin Iran na son a haramta wa jiragen Isra'ila bi ta Hormuz har abada

    Majalisar dokokin Iran ta samar da wani daftarin dokoki kan yadda ƙasar za ta riƙa iko da mashigar Hormuz, kuma ana sa ran kaɗa ƙuri'a kan daftarin a cikin mako mai zuwa.

    Shugaban hukumar kula da ayyuka na majalisar, Mohammed Reza Rezaei Kochi ya ce daftarin ya ƙunshi sauye-sauye kan yadda jiragen ruwa ke ratsawa ta mashigar Hormuz sannan kuma akwai tsarin karɓar kuɗaɗe daga jiragen.

    Mista Kochi ya bayyana wa kafar dillancin labarai ta Fars cewa "ɗaukacin ƴan majalisar za su amince da daftarin sannan daga baya a sanar da fara amfani da shi".

    Bayanai sun nuna cewa daftarin ya ƙunshi wasu matakai guda biyar:

    - Haramcin ratsawar jiragen abokan gaba: Za a haramta wa duk wani jirgin dakon man fetur mai alaƙa da Amurka da Isra'ila ratsawa ta mashigar Hormuz har abada.

    -Karɓar haraji: Za a karɓi kuɗi a matsayin jangali kan aikin yin jagora da tabbatar cewa jiragen ruwa sun ratsa ta wannan mashiga cikin aminci.

    -Tallafa wa takardar kuɗin Iran: A ƙoƙarin bunƙasa darajar takardar kuɗi ta riyal, duk wani jirgi mai ratsawa zai biya jangali ne ta amfani da takardar kuɗin Iran ta Riyal.

    -Amfani da sunan Mashigar Gulf: Za a buƙaci duk wani jirgin da zai ratsa ya yi amfani da asalin sunan da aka san mashigar da shi, wato mashigar Persia a duk takardun da za a cike da kuma bayanan da suke bayarwa na tafiya.

    -Yadda za a kasafta kuɗi: Za a kasafta kuɗaɗen jangali da aka samu kamar haka: Za a kashe kashi 30% wajen ƙarfafa soji da tabbatar da tsaron yanki, sai kuma kashi 70% don inganta rayuwar al'umma.

  5. Tinubu ya jajanta kan kisan sojoji a Borno

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya jajanta wa al'ummar ƙasar kisan da aka yi wa sojoji a wani hari da mayaƙa suka kai kan wani sansanin soji a jihar Borno, arewa maso gabashin ƙasar.

    "Ina miƙa saƙon ta'aziyyata ga iyalan jajirtattun sojojinmu ƙarƙashin jagorancin Birgediya Janar Oseni Omoh Braimah, waɗanda suka rasa rayukansu wajen kare ƙasarmu a jihar Borno," kamar yadda shugaban ya bayyana a wani bayani da ya fitar a jiya Alhamis.

    A ɗaya ɓangare, cikin wata sanarwa, rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun daƙile harin da aka kai kan sansanin soji a garin Benisheik ranar Alhamis, sai dai rundunar ba ta tabbatar ko ƙaryata kashe sojoji ba.

    Wasu mazauna yankin da abin ya faru sun shaida wa BBC cewa babban sojan da ya jagoranci yunƙurin dakile harin Birgediya Janar Oseni Braimah na cikin waɗanda aka kashe.

    Kafar yaɗa labarai ta AFP ta bayar da rahoton kashe babban sojan, inda ta kafa hujja da bayanai daga majiyoyin tattara bayanan sirri, duk da cewa sojojin Najeriya ba su tabbatar da hakan ba.

    Harin na cikin hare-hare na baya-bayan nan da masu iƙirarin jihadi ke kaiwa kan sansanonin soji a arewa maso gabashin Najeriya, inda mayaƙa suka kwashe sama da shekara 10 suna kai hare-hare.

  6. Ko tattaunawar Iran da Amurka a Pakistan za ta yiwu?

    Ana shirye-shiryen tattaunawa tsakanin Iran da Amurka a Pakistan, wadda za ta gudana a cikin ƙarshen mako.

    Sai dai ya zuwa yanzu babu sanarwa a hukumance da ke nuna cewa tawagogin ɓangarorin biyu sun isa Islamabad, birnin da za a yi ganawar.

    Pakistan na ci gaba da kyautata fatan yiwuwar tattaunawar, da kuma fatan cewa za a samu fahimtar juna.

    To amma a halin yanzu kowa jininsa a ƙumba: A wani saƙon da aka wallafa a shafin sada zumunta, kafin daga baya aka goge, ministan tsaron Pakistan ya bayyana Isra'ila a matsayin "tsinuwa ga bil'adama".

    Isra'ila ta ce ba za a amince da irin haka ba daga ƙasar da ta ce za ta yi aikin sasanci.

  7. Yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Iran da Amurka na rawa

    Yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma tsakanin Amurka da Iran na fuskantar barazana, kwana ɗaya gabanin ganawar ƙeƙe-da-ƙeƙe da ake sa ran ɓangarorin biyu za su yi a Pakistan.

    Shugaba Trump na Amurka ya zargi Iran da karya sharuɗɗan yarjejeniyar ta hanyar ƙin buɗe mashigar Hormuz ga jiragen ruwan dakon man fetur.

    Hukumar kula da sufurin ruwa ta duniya ta ce jiragen ruwa ƙalilan ne suka samu damar ratsawa ta mashigar tun bayan cimma yarjejeniyar.

    A ɓangare ɗaya kuma Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare kan Hezbollah a ƙasar Lebanon - abin da Iran ta ce ya saɓa da sharuɗɗan yarjejeniyar.

  8. 'Ba haka muka yi da Iran ba': Trump kan mashigar Hormuz

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya zargi Iran da kin barin jiragen dakon mai su wuce ta mashigin Hormuz, yayin da yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma ke tanga-tangal, kafin hawa teburin sulhu a karshen makon nan a birnin Islamabad na Pakistan.

    A wasu jerin sakonni da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Mista Trump ya ce hakan ya saɓa wa yarjejeniyar da aka cimma, sannan ya gargaɗi Tehran da kada ta ƙaƙaba kuɗin wucewa ga jiragen ruwan.

    Buɗe mashigar Hormuz na daga cikin wani ɓangare na yarjejeniyar, to sai dai jirage tsiraru ne suka samu wucewa tun bayan fara aiki da yarjejeniyar.

    Tun da farko yayin wani jawabi da ya gabatar, jagoran addinin Iran din Ayatollah Mojtaba Khamenei, ya ce a yanzu mashigin na Hormuz ya shiga wani sabon mataki.

    A cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin din kasar, Mojtaba Khamenei ya ce Iran na da yancin daukar fansa kan hare-haren Amurka da Isra’ila, kana za ta kare kawayenta, watau Hezbollah da sauran kungiyoyin yan turjiya a gabas ta tsakya.

    Ƙasar Pakistan ta ce tana da yaƙinin cewa tattaunawar zaman lafiyar da za a yi a Islamabad a karshen wannan mako za ta gudana kamar yadda aka tsara.

  9. Barka da warhaka!

    Barka da zuwa shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa, inda muke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a wannan rana ta Juma'a 10 ga watan Afrilun 2026.

    Za ku iya yin sharhi kan labaran da muke sakawa a shafukanmu na sada zumunta: facebook, X, Instagram da kuma YouTube.

    Sannan ku shiga zaurenmu na BBC Hausa WhatsApp domin samun labarai da ɗumi-ɗumi.