Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Lahadi 15/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Lahadi 15/03/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Mun yi amfani da makamin Sejil karon farko kan Isra'ila - IGRC

    Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta ce ta yi amfani da wasu nau'in makamai masu linzami kan Isra'ila karon farko tun bayan fara wannan yaƙin.

    Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ya fitar ya ce sun yi amfani da makaman ''Khorramshahr, mai nauyin gaske, wanda ke da kawuna biyu da makaman Khyber-Shakan da Qadr da Emad, waɗanda duka masu linzami ne.

    A cewar rundunar makamin Sejil, matsakaicin makamai ne da ake harbawa dada kan doron ƙasa, wanda ke amfani da man fetur, kuma zai iya tafiyar tazarar tsakanin Natanz zuwa Tel Aviv a cikin minti bakwai.

    A dai dai lokacin da rundunar ke fitar da wannan sanarwa, sojojin Isra'ila sun bayyana gano makaman linzami na Iran da suka nufi ƙasar.

    Hare-haren na zuwa ne ƙasa da sa'a biyu bayan bayar da rahoton wasu hare-haren.

  2. MDD ta yi gargaɗin tsanantar yaƙin Darfur

    Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa hare-haren jirage marasa matuƙa na tsananta matsalar tsaro a yankin darfur na Sudan, musamman kan iyakar ƙasar da Chadi.

    Ana ci gaba da kai hare-hare kan cibiyoyin fararen hula, da suka haɗa da asibitoci da kasuwanni da cibiyoyin adana man fetur da ruwan sha, lamarin da ke haifar da ƙaruwar kashe-kashe da tilasta wa mutane barin wuraren.

    Shigar da kayan agaji yankin ya gamu da cikas bayan da a watan Fabrairu aka kai hari kan wata mota mai ɗauke da kayan agaji daga shirin Samar da Abinci na Majalisar Dinkin Duniya.

    Yayin da yaƙin basasar Sudan ke ci gaba da gudana, fiye da mutum 500,000 aka raba da muhallansu, waɗanda a yanzu ke zama a Tawila.

  3. Iran ta bayar da damar tattaunawa da ƙasashen da ke son buɗe musu mashigar Hormuz

    Ministan harkokin wajen Iran ya ce ƙasarsa ba ta neman dakatar da yaƙi tsakaninta da Amurka da Isra'ila, yayin da ta ci gaba da kai hare-hare a rana ta 16 da fara yaƙin.

    Yayin wata hra da kafar yaɗa labarai ta CBS News, Abbas Araghchi ya ce a shirye Iran take ta kare kanta iya yadda za ta iya, kuma ba ta neman wata tattaunawa da Amurka.

    Tun da farko, ya nuna cewa a shirye Iran take ta shiga tattaunawar da za ta kai ga cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin..

    Isra'ila ta ce za ta faɗaɗa hare-harenta, yayin da sojojin Amurka suka ce ƙarfin sojin Iran na raguwa.

    Amma kuma Iran na ci gaba da hare-haren martani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan sansanonin sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya.

  4. Makamin linzami mai ƴaƴa na Iran ya faɗa wani gida a Isra'ila

    Wani makamai mai linzami mai ƴaƴa da Iran ta harba cikin Isra'ila ya faɗa kan wani gida a kusa da Tel Aviv, babban birnin ƙasar.

    Harin ya haifar da ɓarna, sai babu labarin rasa rai.

    Tun da farko Isra'ila ta ce ta ƙaddamar da manyan hare-hare a yammacin Iran, kan abin da ta kira cibiyoyin gwamnati.

    Kakakin IDF Burgediya Janar Effie Defrin ya ce sojojin Isra'ila na shirin ɗaukar aƙalla mako uku nan gaba tana ƙaddamar da hare-hare cikin Iran.

    A nata ɓangare rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta sha alwashin farauto tare da kashe Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.

  5. 'Mutanen da suka mutu a Lebanon sun kai 850'

    Ma'aikatar lafiyar Lebanon ta ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren Isra'ila tun bayan fara yaƙin Iran ya kai 850.

    An fara ƙidaya wannan adadi daga ranar 2 ga watan Maris, lokacin da Isra'ila ta ƙaddamar da hare-hare a Lebanon bayan da ƙungiyar Hezbollan ta harba makaman roka zuwa ƙasar.

  6. Hotunan ɓarnar hare-haren Isra'ila a Iran

    An samu fitowar sabbin hotunan ɓarnar hare-haren Isra'ila a Iran.

    Iraniyawa na share ɓaraguzan gidajen da suka lalace a Tehran, babban birnin ƙasar.

    Tun da farko Isra'ila ta ce ta ƙaddamat da ''manyan hare-hare a yammacin Iran, sai dai har yanzu babu labarin ɓarnar da suka haifar.

  7. Isra'ilawa fiye da 100 aka kai asibiti cikin sa'a 24 - Ma'aikatar lafiyar ƙasar

    Ma'aikatar lafiyar Isra'ila ta ce mutum 108 ne aka kai asibiti sakamakon raunukan da suka samu a cikin sa'o'i 24.

    Ta ce daga cikin wannan adadi, 96 sun samu ƙananan raunuka, biyu na cikin matsakaicin yanyi, yayain da tara ke buƙatar gwaje-gwaje.

    Tun bayan fara musayar hare-hare tsakanin Isra'ila da Iran, ma'aikatar lafiyar Isra'ila ta ce mutum 3,195 ne aka kai asibiti domin yi musu maganin raunukan da suka samu, sakamakon hare-haren makamai masu linzami da Iran ke kai wa ƙasar.

    Ma'aikatar lafiyar Isra'ilar ba ta bayar da rahoton adadin mutanen da suka mutu.

  8. Ɓarnar da hare-haren cikin dare suka yi a Holon na Isra'ila

    An samu sabbin hotunan da ke nuna ɓarnar da hare-haren cikin dare suka yi a birnin holon da ke kudancin Tel Aviv, a Isra'ila.

    An ga yadda wata mota ta kife, yayin da ɓaraguzai suka warwatsu, sai kuma wani ƙaton rami da hari ya haifar a kusa da wani gina.

    Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar (MDA) ta ce ta yi wa wasu mutum biyu da suka jikkata a hare-haren maganin ƙananan raunukan da suka samu.

    Wani tsoho mai shekara 80 ya samu raunukan tsagewar gilashi, yayin da wata tsohuwa mai shekara 80 ta samu matsalar numfashi saboda shkara hayaƙi.

    An kuma kwantar wa mutane da dama hankali da suka firgita a lokacin harin, a cewar hukumar ta MDA.

  9. Iran ta sha alwashin 'farautar' Netanyahu domin 'kashe' shi

    Sojojin Iran sun sha alwashinkashe firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, kamar yadda kafofin yaɗa labaran Iran suka ruwaito.

    Kamfanin dillancin labarai na Mehr ya ce dakarun juyin juya halin ƙasar za su ''ci gaba da farautar Netanyahu domin kashe shi da ƙarfin tsiya''

    Rundunar ta IRGC ta yi ikirarin cewa ta kai hare-hare cikin Isra'ila da sansanonin sojin Amurka uku a yanzkin Gabas ta Tsakiya a karo na 52 na hare-haren da ta ƙaddamar.

  10. Mojtaba Khamenei 'na cikin ƙoshin lafiya' - Araghchi

    Ministan harkkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce sabon jagoran addinin ƙasar, Mojtaba Khamenei na cikin ƙoshin lafiya.

    Cikin wata hira da kafar yaɗa labarai ta Alaraby Aljadeed ya ce sabon jagoran addinin na ''cikin yanayin cikakken iko da ƙasar''.

    • Sabon jagoran dai, bai bayyana a bainar jama'a ba tun bayan naɗa shi a matsayin ranar 8 ga watan Maris. Sai dai a ranar 12 ga watan Maris an yaɗa jawabinsa ta kafofin yaɗa labaran ƙasar.

    Ya ce Iran na maraba da ''yunƙarin ƙasashen Gabas ta Tsakiya na kawo ƙarshen yaƙin''.

    Abbas Araghchi ya ce Iran za ta buɗe mashigar Hormuz amma ban da jiragen ruwan Amurka da ƙawayenta.

    Sai dai Araghchi ya ce ''zuwa yanzu babu wani yunƙuri na kawo ƙarshen yaƙin''.

  11. Labarai da dumi-dumi, Iran ta sake harba makamai masu linzami zuwa Isra'ila

    Rundunar sojin Isra'ila (IDF) ta fitar da sabon gargaɗi ga ƴan ƙasar, tana mai cewa ta hango makamai masu linzami da OIran ta harba cikin ƙasar.

    Hare-haren su ne na biyar da Iran ta ƙaddamar cikin Isra'ila a cikin sa'o'i tara.

    Sojojin Isra'ilar sun buƙaci ƴanƙasar da ke zaune a wuraren da makaman suka hara su nemi mafaka.

  12. 'An kai hari sansanonin sojin Amurka a Iraƙi'

    Jami'an tsaro a Iraƙi sun ce an kai harin jiragen sama marassa matuƙa kan wani sansanin sojin Amurka da ke kusa da filin jirgin sama na Bagadaza, babban birnin ƙasar.

    Rahotanni sun ce wuta ta tashi ganga-ganga a sansanin, amma ba a ji komai ba game da ko harin ya jikkata ko halaka wasu.

    An kai harin ne ƴan sa'o'i bayan da ofishin jakadancin Amurka a Bagadazan ya yi kira ga dukkanin Amurkawa da har yanzu ke ƙasar Iraƙi su fice nan take.

    A ranar Juma'ar da ta gabata ma an kai hari da jiragen sama marassa matuƙa kan ofishin jakadancin na Amurka da ke Bagadazan.

    Ofishin ya ce ƙungiyoyin ƴanbindiga da ke goyon bayan Iran, suna kai wa wuraren da ke da alaka da Amurka hari na makaman roka da jirage marasa matuka a Iraƙi.

  13. Iran ta yi barazanar faɗaɗa yaƙi a yankin Gabas ta Tsakiya

    Iran ta yi barazanar ta faɗaɗa yaƙin da take yi zuwa maƙwabtan ƙasashe, inda ta yi kira ga Hadaddiyar Daular Larabawa ta fara kwashe ƴan ƙasarta daga yankunan da ke kusa da tashoshin jiragen ruwa a Abu Dhabi da Dubai da kuma Fujairah.

    Yayin da rikicin ya shiga mako na uku, Iran ta ci gaba da harba muggan makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan kayayyaki da cibiyoyi na ƙasashe makwabtanta da kuma Isra'ila.

    Duk da ruwan bama-bamai ba ƙaƙƙautawa tsawon mako biyu na sojojin Amurka da suka fi ƙarfi ainun, Iran ta ci gaba da ƙaddamar da hare-hare.

    Wani mai bayar da shawara na diflomasiyya ga shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa, ya mayar da martani da cewa ƙasarsa tana da ƴancin kare kanta, amma ta zaɓi ta ci gaba da amfani da hankali da tunani.

    An ji fashewar bama-bamai a Manama, babban birnin ƙasar Bahrain.

  14. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da hutun karshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku ci gaba da tafka muhara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.